< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
Zoper Moáb tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog: »Gorje Nebóju! Kajti ta je oplenjen. Kirjatájim je zbegan in zavzet. Misgab je zbegan in zaprepaden.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
Moábove hvale ne bo več. V Hešbónu so snovali zlo zoper njega; pridimo in iztrebimo ga pred tem, da bi bil narod. Tudi ti boš iztrebljen, o Madmén; meč te bo preganjal.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
Glas vpitja bo iz Horonájima, plenjenje in veliko uničenje.
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Moáb je uničen; njegovi malčki so storili, da se je slišal jok.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
Kajti ob vzpenjanju Luhíta se bo vzdigovalo nenehno jokanje, kajti ob spuščanju Horonájima so sovražniki slišali krik pogube.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
Pobegnite, rešite svoja življenja in bodite podobni brinu v divjini.
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
Kajti ker si zaupal v svoja dela in svoje zaklade, boš tudi ti zajet. Kemoš bo šel naprej v ujetništvo skupaj s svojimi duhovniki in svojimi princi.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
Plenilec bo prišel nad vsako mesto in nobeno mesto ne bo uteklo. Tudi dolina bo propadla in ravnina bo uničena, kakor je govoril Gospod.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Daj peruti Moábu, da bo lahko pobegnil in ušel, kajti njegova mesta bodo zapuščena, brez kogarkoli, da bi v njih prebival.
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Preklet bodi, kdor dela Gospodovo delo varljivo in preklet bodi, kdor svoj meč zadržuje od krvi.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
Moáb je bil sproščen od svoje mladosti in se ustalil na svojih drožeh in ni bil izpraznjen iz posode v posodo niti ni šel v ujetništvo. Zato bo njegov okus ostal v njem in njegova vonjava ni spremenjena.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
Zato, glej, prihajajo dnevi, ‹ govori Gospod, ›ko bom k njemu poslal postopače, ki mu bodo povzročili, da se potepa in izpraznili bodo njegove posode in počili njihove mehove.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
Moáb se bo sramoval Kemoša, kakor se je Izraelova hiša sramovala Betela, njihovega zaupanja.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
Kako pravite: ›Mi smo mogočni in močni možje za vojno?‹
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
Moáb je oplenjen in odšel gor iz svojih mest in njegovi izbrani mladeniči so odšli dol k pokolu, ‹ govori Kralj, katerega ime je Gospod nad bojevniki.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
Blizu je Moábova katastrofa, da pride in njegova stiska silno hiti.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
Vsi vi, ki ste okoli njega, žalujte za njim; in vsi vi, ki poznate njegovo ime, recite; ›Kako je močna opora zlomljena in krasna palica!‹
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
Ti hči, ki poseljuješ Dibón, pridi dol iz svoje slave in sédi v žeji; kajti plenilec Moába bo prišel nadte in ta bo uničil tvoja oporišča.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
Oh prebivalec Aroêrja, stoj ob poti in oprezaj; in vprašaj tistega, ki beži in tisto, ki pobegne ter reci: ›Kaj se je zgodilo?‹
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
Moáb je zbegan, kajti zlomljen je. Tulite in vpijte. Povejte v Arnónu, da je Moáb oplenjen.
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
Sodba je prišla nad ravno deželo; nad Holón, nad Jahac, nad Mefáat,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
nad Dibón, nad Nebó, nad Bet Diblatájim,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
nad Kirjatájim, nad Bet Gamúl, nad Bet Meón,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
nad Kerijót, nad Bocro in nad vsa mesta moábske dežele, daljna ali bližnja.
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
Moábov rog je odsekan in njegov laket je zlomljen, ‹ govori Gospod.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
›Opijanite ga, kajti poveličal se je zoper Gospoda. Tudi Moáb se bo valjal v svojem izbljuvku in tudi on bo v posmeh.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
Mar vam ni bil Izrael v posmeh? Je bil najden med tatovi? Kajti odkar govoriš o njem, poskakuješ od veselja.
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
Oh vi, ki prebivate v Moábu, zapustite mesta in prebivajte na skali in bodite podobni golobici, ki dela svoje gnezdo na straneh ustja luknje.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
Slišali smo ponos Moába (on je silno ponosen), njegovo nadutost, njegovo aroganco, njegov ponos in oholost njegovega srca.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
Poznam njegov bes, ‹ govori Gospod; ›toda to ne bo tako; njegove laži na to ne bodo tako vplivale.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
Zato bom tulil zaradi Moába in vpil zaradi vsega Moába; moje srce bo žalovalo zaradi mož iz Kir Hêresa.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
Oh sibmanska trta, jokal bom za teboj z jokanjem Jazêrja. Tvoje rastline so odšle prek morja, segle so celó k jazêrskemu morju. Plenilec je padel na tvoje poletne sadove in na tvojo trgatev.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
Radost in veselje sta vzeta iz obilnega polja moábske dežele. Trti sem velel, da odpove pred vinskimi stiskalnicami. Nihče ne bo mendral z vriskanjem; njihovo vriskanje ne bo vriskanje.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
Od krika Hešbóna, celó do Elaléja in celó do Jahaca so izgovarjali svoj glas, od Coarja celó do Horonájima, kakor triletna telica, kajti tudi nimrímske vode bodo zapuščene.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
Poleg tega bom povzročil, da odneha v Moábu, ‹ govori Gospod, ›kdor daruje na visokih krajih in kdor zažiga kadilo svojim bogovom.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
Zato bo moje srce ihtelo kakor piščali za Moábom in moje srce bo ihtelo kakor piščali za možmi Kir Hêresa, ker so bogastva, ki jih je pridobil, izginila.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
Kajti vsaka glava bo plešasta in vsaka brada pristrižena. Na vseh rokah bodo vrezi in na ledjih vrečevina.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
Tam bo splošno žalovanje na vseh hišnih strehah Moába in na njegovih ulicah, kajti zlomil sem Moáb kakor posodo, v kateri ni zadovoljstva, ‹ govori Gospod.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Tulili bodo, rekoč: »Kako je ta zlomljen! Kako je Moáb s sramoto obrnil hrbet! Tako bo Moáb v posmeh in zaprepadenost vsem okoli njega.‹
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
Kajti tako govori Gospod: ›Glej, letel bo kot orel in svoje peruti bo širil nad Moábom.
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Kerijót je zavzet, oporišča so presenečena in srca mogočnih mož v Moábu bodo na ta dan kakor srce ženske v njenih ostrih bolečinah.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
Moáb bo uničen pred tem, da bi bil ljudstvo, ker se je poveličeval zoper Gospoda.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
Strah, jama in zanka bodo nad teboj, oh prebivalec Moába, ‹ govori Gospod.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
›Kdor beži pred strahom, bo padel v jamo, in kdor vstaja iz jame, bo zajet v zanko, kajti jaz bom to privedel nadenj, celó nad Moáb, leto njihovega obiskanja, ‹ govori Gospod.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
›Tisti, ki so zbežali, so stali pod hešbónsko senco zaradi sile. Toda ogenj bo izšel iz Hešbóna, plamen iz srede Sihóna in použil bo Moábov kot in tême upornih.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
Gorje tebi, oh Moáb! Ljudstvo Kemoša se pogublja, kajti tvoji sinovi so zajeti [kot] ujetniki in tvoje hčere [kot] ujetnice.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
Vendar bom v zadnjih dneh ponovno privedel Moábovo ujetništvo, ‹ govori Gospod. ›Tako daleč je sodba od Moába.‹«

< Irmiya 48 >