< Irmiya 48 >
1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
О Моаве тако рече Господь Вседержитель, Бог Израилев: о, люте Нававу, яко погибе, взяся Кариафаим, посрамися Масигаф и побежден есть.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
Несть ктому целение в Моаве, веселие во Есевоне, помыслиша нань злая: приидите и потребим я от язык: (сего ради) молчя умолкнеши, пойдет за тобою мечь.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
Глас вопля от Оронаима, погубление и сотрение велико.
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Сотреся Моав, возвестите вопль малых его.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
Яко исполнися Алаоф плача: взыдет рыдая путем Оронаима, врази, вопль сотрения слышасте.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
Бежите и спасите душы вашя, и будете яко осел дивий в пустыни.
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
Понеже имел еси надежду во оградах твоих и в сокровищих твоих, и ты ят будеши: и пойдет Хамос во преселение, и священницы его и князи его вкупе.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
И приидет губитель на всяк град, и не избавится ни един град, и погибнут удолия, и погубятся поля, якоже рече Господь.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Дайте знамение Моаву, яко прикосновением прикосновен будет, и вси гради его будут пусти и без живущих.
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Проклят (человек) творяй дело Господне с небрежением, и проклят возбраняяй мечу своему от крове.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
Почиваше Моав от младости своея и бе уповая на славу свою: не прелияся от сосуда в сосуд и во преселение не отиде: сего ради пребысть вкус его в нем, и воня его несть пременена.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
Сего ради, се, дние грядут, глаголет Господь, и послю ему преселители, и преселят его, и сосуды его истощат и роги его сокрушат:
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
и посрамится Моав от Хамоса, якоже посрамлен есть дом Израилев от Вефиля, в немже имяху надежду.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
Како глаголете: сильни есмы и мужие крепцы во бранех?
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
Погибе Моав, град его, и избраннии юноши его снидоша под мечь, глаголет Царь, Господь Вседержитель имя Его.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
Близ день Моавль, еже приити, и зло его скоро зело.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
Утешайте его вси, иже окрест его, и вси ведящии имя его: рцыте, како сокрушися жезл крепости, палица славна?
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
Сниди от славы и сяди, во влаге живущая, дщи Дивоня, яко губитель Моавский взыдет на тя разрушаяй ограды твоя.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
На пути стани и воззри, живущая во Ароире, и вопроси бежащаго и избегшаго, и рцы: что се бысть?
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
Посрамися Моав, зане побежден есть: рыдайте и вопийте, возвестите во Арноне, яко погибе Моав,
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
и суд прииде на землю напольную, на Хелон и на Рефас и на Мофаф,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
и на Девон и на Наво и на дом Девлафаим,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
и на Кариафаим и на Вефгамул и на дом Маонов,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
и на Кариоф и на Восора и на вся грады Моавли, иже далече и иже близ суть.
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
Отсечен есть рог Моавль, и мышца его сокрушися, глаголет Господь:
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
упойте его, яко на Господа возвеличися, и приразит Моав руку свою (о блевотину), и будет в посмех и сам.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
И аще не в посмех бысть тебе Израиль, аще в татстве твоем обретеся, яко воевал еси его: преселишися инамо.
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
Оставите грады и пребывайте на камени, живущии в Моаве, и будите якоже голуби гнездящиися в каменех, во устех скважни.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
Слышахом гордость Моавлю, горд бе зело: презорство его и кичение его, возношение и воздвижение сердца его.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
Аз же вем дела его, глаголет Господь: не доволство ли его тако сотвори?
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
Сего ради над Моавом возрыдайте всюду, возопийте над мужи Кирады смущения.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
Яко плачем Иазировым восплачуся о тебе, винограде Асеримль! Леторасли твоя проидоша море, градов Иазировых коснушася, на жатву твою и на винное собирание твое хищник нападе.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
Отята есть радость и веселие от Кармила и от земли Моавли, и вино от точил отях: никакоже изгнетаяй винну ягоду по обычаю песни воспоет.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
От вопля Есевонска даже до Елеала и Иаса грады их даша глас свой, от Сигора даже до Оронаима, и юница трилетная, понеже и воды Немрим во сожжение будут.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
И отиму Моава, глаголет Господь, жрущаго на горах и кадящаго богом своим.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
Того ради сердце Моава, яко цевницы звяцати будут, и сердце мое к мужем Кирады яко цевница звяцати будет: сего ради, яже пристяжа, погибоша от человек.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
Всяка бо глава на всяцем месте острижена будет, и всяка брада оброснется, и всяка рука посечена будет, и на всяцем чресле вретище,
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
и на всех храминах Моавских и на стогнах его всяк плачь, понеже сокруших Моава, якоже сосуд непотребен, глаголет Господь.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Како изменися? Возрыдаша, како обрати хребет Моав и посрамися? И бысть Моав в посмех и в ненависть всем окрест себе.
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
Яко тако глаголет Господь: се, якоже орел полетит и распрострет криле свои на Моава,
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
взят есть Кариоф, и ограды его обстоимы суть: и будет сердце сильных Моавских в той день, яко сердце жены родящия.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
И погибнет Моав от людий, яко на Господа возвеличися.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
Страх и пропасть и сеть на тя, о, живущий в Моаве, глаголет Господь.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
Иже убежит от лица страха, впадет в пропасть: и излазяй из пропасти имется сетию: понеже наведу сия на Моава в лето посещения их, глаголет Господь.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
Во стени Есевонстей сташа от силы избегше, огнь бо изыде от Есевона и пламень от среды Сеона, и пожже часть Моава и верх сынов смятения.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
Горе тебе, Моаве! Погибоша людие Хамоса, яко отведошася сынове твои и дщери твоя в плен.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
И возвращу плен Моавль в последния дни, глаголет Господь. До зде суд Моавль.