< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
Contra Moab assim diz o Senhor dos Exercitos, Deus de Israel: Ai de Nebo, porque foi destruida: envergonhada está Kiriathaim, já é tomada: Misgab está envergonhada e espantada.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
Já não ha mais gloriação de Moab ácerca de Hesbon; pensaram mal contra ella, dizendo: Vinde, e desarreiguemol-a, para que não seja mais povo; tambem tu, ó Madmen, serás desarreigada; a espada te irá seguindo
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
Voz de grito de Horonaim: ruina e grande destruição.
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Já está destruida Moab: seus filhinhos fizeram-se ouvir com gritos.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
Porque na subida de Luhith subirá choro sobre choro; porque na descida de Horonaim os adversarios de Moab ouviram um lastimoso clamor.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
Fugi, salvae a vossa vida, e sereis como a tamargueira no deserto.
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
Porque, por causa da tua confiança nas tuas obras, e nos teus thesouros, tambem tu serás tomada; e Camos sairá para o captiveiro, os seus sacerdotes e os seus principes juntos.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
Porque virá o destruidor sobre cada uma das cidades, e nenhuma escapará, e perecerá o valle, e destruir-se-ha a campina; porque o Senhor o disse.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Dae azas a Moab; porque voando sairá, e as suas cidades se tornarão em assolação, e ninguem morará n'ellas.
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Maldito aquelle que fizer a obra do Senhor fraudulosamente: e maldito aquelle que veda a sua espada do sangue.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
Moab esteve descançado desde a sua mocidade, e repousou nas suas fezes, e não foi trafegado de vaso em vaso, nem foi para o captiveiro; por isso permaneceu o seu sabor n'elle, e o seu cheiro não mudou.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
Portanto, eis que dias veem, diz o Senhor, em que lhe enviarei andantes, que o farão andar a grandes passos; e despejarão os seus vasos, e romperão os seus odres.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
E Moab terá vergonha de Camos, como se envergonhou a casa de Israel de Beth-el, sua confiança.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
Como direis, pois: Valentes somos e homens fortes para a guerra?
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
Já está destruido Moab, e subiu das suas cidades, e os seus mancebos escolhidos desceram á matança, diz o rei, cujo nome é o Senhor dos Exercitos.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
Já é chegada a vinda da perdição de Moab; e apressura-se muito o seu mal
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
Condoei-vos d'elle todos os que estaes em redor d'elle, e todos os que sabeis o seu nome: dizei: Como se quebrou a vara forte, o cajado formoso?
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
Desce da tua gloria, e assenta-te em secco, ó moradora, filha de Dibon; porque já o destruidor de Moab subiu contra ti, e já desfez as tuas fortalezas.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
Põe-te no caminho, e espia, ó moradora de Aroer: pergunta ao que vae fugindo; e á que escapou dize: Que succedeu?
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
Moab está envergonhado, porque foi quebrantado; uivae e gritae: annunciae em Arnon que já Moab está destruido.
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
Tambem o juizo veiu sobre a terra da campina: sobre Holon, e sobre Jaza, e sobre Mephaat,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
E sobre Dibon, e sobre Nebo, e sobre Beth-diblataim,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
E sobre Kiriathaim, e sobre Beth-gamul, e sobre Beth-meon,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
E sobre Kerioth, e sobre Bozra; e até sobre todas as cidades da terra de Moab, as de longe e as de perto.
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
Já é cortado o corno de Moab, e é quebrantado o seu braço, diz o Senhor.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
Embriagae-o, porque contra o Senhor se engrandeceu; e Moab se revolverá no seu vomito, e elle tambem será por escarneo.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
Porque não te foi tambem Israel por escarneo? porventura foi achado entre ladrões, porque desde que fallas d'elle te ris?
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
Deixae as cidades, e habitae no rochedo, ó moradores de Moab; e sêde como a pomba que se aninha nas extremidades da bocca da caverna.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
Já ouvimos a soberba de Moab, que é soberbissimo, como tambem a sua arrogancia, e a sua soberba, e sua altivez e a altura do seu coração.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
Eu conheço, diz o Senhor, a sua indignação, porém assim não será: as suas mentiras não o farão assim.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
Por isso uivarei por Moab, e gritarei por todo o Moab: pelos homens de Kir-heres gemerão.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
Com o choro de Jaezar chorar-te-hei, ó vide de Sibma; já os teus ramos passaram o mar, e chegaram até ao mar de Jaezer; porém o destruidor caiu sobre os fructos do teu verão, e sobre a tua vindima.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
Tirou-se pois o folguedo e a alegria do campo fertil e da terra de Moab; porque fiz cessar o vinho dos lagares: já não pisarão uvas com jubilo: o jubilo não será jubilo.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
Por causa do grito de Hesbon até Eleale e até Jahaz, deram a sua voz desde Zoar, até Horonaim, como bezerra de tres annos; porque até as aguas do Nimrim se tornarão em assolações.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
E farei cessar em Moab, diz o Senhor, quem sacrifique no alto, e queime incenso aos seus deuses.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
Por isso resoará o meu coração por Moab como frautas; tambem resoará o meu coração pelos homens de Kir-heres como frautas; porquanto a abundancia que ajuntou se perdeu.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
Porque toda a cabeça será calva, e toda a barba será diminuida; sobre todas as mãos ha sarjaduras, e sobre os lombos saccos.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
Sobre todos os telhados de Moab e nas suas ruas haverá um pranto geral; porque quebrantei a Moab, como a um vaso que não agrada, diz o Senhor.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Como foi quebrantado? uivam: como virou Moab as costas e se envergonhou? assim será Moab objecto de escarneo e de espanto a todos os que estão em redor d'elle.
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
Porque assim diz o Senhor: Eis que voará como a aguia, e estenderá as suas azas sobre Moab.
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Já são tomadas as cidades, e occupadas as fortalezas: e será o coração dos valentes de Moab n'aquelle dia como o coração da mulher que está com dôres de parto
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
E Moab será destruido, para que não seja povo; porque se engrandeceu contra o Senhor.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
Temor, e cova, e laço, veem sobre ti, ó morador de Moab, diz o Senhor.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
O que fugir do temor cairá na cova, e o que subir da cova ficará preso no laço; porque trarei sobre elle, sobre Moab, o anno da sua visitação, diz o Senhor.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
Os que fugiam da força pararam á sombra de Hesbon; porém fogo saiu de Hesbon, e a labareda do meio de Sihon, e devorou o canto de Moab e a mioleira dos filhos de arroido.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
Ai de ti, Moab; já pereceu o povo de Camos; porque teus filhos foram levados em captiveiro, como tambem tuas filhas em captividade.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
Porém farei voltar os captivos de Moab no ultimo dos dias, diz o Senhor. Até aqui o juizo de Moab.

< Irmiya 48 >