< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
درباره موآب، یهوه صبایوت خدای اسرائیل چنین می‌گوید: «وای بر نبوزیرا که خراب شده است. قریه تایم خجل وگرفتار گردیده است. و مسجاب رسوا و منهدم گشته است.۱
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
فخر موآب زایل شده، در حشبون برای وی تقدیرهای بد کردند. بیایید و او رامنقطع سازیم تا دیگر قوم نباشد. تو نیز‌ای مدمین ساکت خواهی شد و شمشیر تو را تعاقب خواهدنمود.۲
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
آواز ناله از حورونایم مسموع می‌شود. هلاکت و شکستگی عظیم.۳
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
موآب بهم شکسته است و صغیرهای او فریاد برمی آورند.۴
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
زیرا که به فراز لوحیت با گریه سخت برمی آیند و ازسرازیری حورونایم صدای شکست یافتن ازدشمنان شنیده می‌شود.۵
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
بگریزید و جانهای خود را برهانید و مثل درخت عرعر در بیابان باشید.۶
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
زیرا از این جهت که به اعمال و گنجهای خویش توکل نمودی تو نیز گرفتار خواهی شد. وکموش با کاهنان و سرورانش با هم به اسیری خواهند رفت.۷
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
و غارت کننده به همه شهرهاخواهد آمد و هیچ شهر خلاصی نخواهد یافت وبرحسب فرمان خداوند اهل وادی تلف خواهندشد و اهل همواری هلاک خواهند گردید.۸
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
بالهابه موآب بدهید تا پرواز نموده، بگریزد وشهرهایش خراب و غیرمسکون خواهد شد.۹
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
ملعون باد کسی‌که کار خداوند را با غفلت عمل نماید و ملعون باد کسی‌که شمشیر خود را از خون باز‌دارد.۱۰
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
موآب از طفولیت خودمستریح بوده و بر دردهای خود نشسته است و ازظرف به ظرف ریخته نشده و به اسیری نرفته است. از این سبب طعمش در او مانده است وخوشبویی او تغییر نیافته است.۱۱
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
بنابراین اینک خداوند می‌گوید: روزها می‌آید که من ریزندگان می‌فرستم که او را بریزند و ظروف او را خالی کرده، مشکهایش را پاره خواهند نمود.۱۲
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
وموآب از کموش شرمنده خواهد شد چنانکه خاندان اسرائیل از بیت ئیل که اعتماد ایشان بود، شرمنده شده‌اند.۱۳
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
چگونه می‌گویید که ماشجاعان و مردان قوی برای جنگ می‌باشیم؟۱۴
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
موآب خراب شده دود شهرهایش متصاعدمی شود و جوانان برگزیده‌اش به قتل فرودمی آیند. پادشاه که نام او یهوه صبایوت می‌باشداین را می‌گوید:۱۵
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
رسیدن هلاکت موآب نزدیک است و بلای او بزودی هر‌چه تمامتر می‌آید.۱۶
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
‌ای جمیع مجاورانش و همگانی که نام او رامی دانید برای وی ماتم گیرید. بگویید عصای قوت و چوبدستی زیبایی چگونه شکسته شده است!۱۷
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
‌ای دختر دیبون که (در امنیت ) ساکن هستی از جلال خود فرود آی و در جای خشک بنشین زیرا که غارت کننده موآب بر تو هجوم می‌آورد و قلعه های تو را منهدم می‌سازد.۱۸
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
‌ای تو که در عروعیر ساکن هستی به‌سر راه بایست ونگاه کن و از فراریان و ناجیان بپرس و بگو که چه شده است؟۱۹
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
موآب خجل شده، زیرا که شکست یافته است پس ولوله و فریاد برآورید. در ارنون اخبار نمایید که موآب هلاک گشته است.۲۰
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
و داوری بر زمین همواری رسیده است.۲۱
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
و بر دیبون و نبوو بیت دبلتایم،۲۲
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
و بر قریه تایم و بیت جامول وبیت معون،۲۳
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
و بر قریوت و بصره و بر تمامی شهرهای بعید و قریب زمین موآب.۲۴
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
«خداوند می‌گوید که شاخ موآب بریده وبازویش شکسته شده است.۲۵
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
او را مست سازیدزیرا به ضد خداوند تکبر می‌نماید. و موآب درقی خود غوطه می‌خورد و او نیز مضحکه خواهدشد.۲۶
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
آیا اسرائیل برای تو مضحکه نبود؟ و آیااو در میان دزدان یافت شد به حدی که هر وقت که درباره او سخن می‌گفتی سر خود رامی جنبانیدی؟۲۷
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
‌ای ساکنان موآب شهرها راترک کرده، در صخره ساکن شوید و مثل فاخته‌ای باشید که آشیانه خود را در کنار دهنه مغاره می‌سازد.۲۸
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
غرور موآب و بسیاری تکبر او را وعظمت و خیلا و کبر و بلندی دل او را شنیدیم.۲۹
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
خداوند می‌گوید: خشم او را می‌دانم که هیچ است و فخرهای او را که از آنها هیچ برنمی آید.۳۰
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
بنابراین برای موآب ولوله خواهم کرد و به جهت تمامی موآب فریاد برخواهم آورد. برای مردان قیرحارس ماتم گرفته خواهد شد.۳۱
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
برای تو‌ای مو سبمه به گریه یعزیر خواهم گریست. شاخه های تو از دریا گذشته بود و به دریاچه یعزیر رسیده، بر میوه‌ها و انگورهایت غارت کننده هجوم آورده است.۳۲
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
شادی وابتهاج از بستانها و زمین موآب برداشته شد وشراب را از چرخشتها زایل ساختم و کسی آنهارا به صدای شادمانی به پا نخواهد فشرد. صدای شادمانی صدای شادمانی نیست.۳۳
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
به فریادحشبون آواز خود را تا العاله و یاهص بلند کردندو از صوغر تا حورونایم عجلت شلیشیا، زیرا که آبهای نمریم نیز خرابه شده است.۳۴
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
و خداوند می گوید من آنانی را که در مکان های بلند قربانی می‌گذرانند و برای خدایان خود بخورمی سوزانند از موآب نابود خواهم گردانید.۳۵
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
لهذا دل من به جهت موآب مثل نای صدامی کند و دل من به جهت مردان قیرحارس مثل نای صدا می‌کند، چونکه دولتی که تحصیل نمودند تلف شده است.۳۶
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
و هر سر بی‌مو گشته وهر ریش تراشیده شده است و همه دستهاخراشیده و بر هر کمر پلاس است.۳۷
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
بر همه پشت بامهای موآب و در جمیع کوچه هایش ماتم است زیرا خداوند می‌گوید موآب را مثل ظرف ناپسند شکسته‌ام.۳۸
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
چگونه منهدم شده و ایشان چگونه ولوله می‌کنند؟ و موآب چگونه به رسوایی پشت داده است؟ پس موآب برای جمیع مجاوران خود مضحکه و باعث ترس شده است.۳۹
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
زیرا خداوند چنین می‌گوید: او مثل عقاب پرواز خواهد کرد و بالهای خویش را بر موآب پهن خواهد نمود.۴۰
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
شهرهایش گرفتار وقلعه هایش تسخیرشده، و دل شجاعان موآب درآن روز مثل دل زنی که درد زه داشته باشد خواهدشد.۴۱
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
و موآب خراب شده، دیگر قوم نخواهدبود چونکه به ضد خداوند تکبر نموده است.۴۲
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
خداوند می‌گوید: ای ساکن موآب خوف وحفره و دام پیش روی تو است.۴۳
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
آنکه از ترس بگریزد در حفره خواهد افتاد و آنکه از حفره برآید گرفتار دام خواهد شد، زیرا خداوندفرموده است که سال عقوبت ایشان را بر ایشان یعنی بر موآب خواهم آورد.۴۴
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
فراریان بی‌تاب شده، در سایه حشبون ایستاده‌اند زیرا که آتش ازحشبون و نار از میان سیحون بیرون آمده، حدودموآب و فرق سر فتنه انگیزان را خواهد سوزانید.۴۵
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
وای بر تو‌ای موآب! قوم کموش هلاک شده‌اند زیرا که پسرانت به اسیری و دخترانت به جلای وطن گرفتار گردیده‌اند.۴۶
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
لیکن خداوندمی گوید که در ایام آخر، اسیران موآب را بازخواهم آورد. حکم درباره موآب تا اینجاست.»۴۷

< Irmiya 48 >