< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
This is a message about Moab. The Commander of the armies of angels said: “Terrible things will happen to Nebo [town]; it will [soon] be ruined. Kiriathaim [city] will be captured and [all its people will be] humiliated; the high wall around their city will be ruined, and [its people] will become ashamed.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
No one will boast about Moab again; the [enemies of Moab] will plan to destroy [the capital city, ] Heshbon. [They will say, ] ‘Come, let’s cause Moab to no longer be a nation.’ You people in Madmen [town], you also will be silenced; enemy armies [MTY] will pursue you.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
Listen to the people of Horonaim [town] screaming; [they will be wailing because their town will have been] devastated and destroyed [DOU].
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
[All of] Moab will be ruined; [even] the little children will cry [loudly].
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
They will cry bitterly as they climb up Luhith [Hill]. [Others will wail] on the road down to Horonaim, being very sad because of [their town being] destroyed.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
[Someone will say to them], ‘Flee! Hide in the desert!’
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
But you trusted that because you were rich and powerful, [you would be safe]; so you will be captured. [The statue of your god] Chemosh and all his priests and officials will be taken away to distant lands.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
All the towns [in Moab] will be destroyed; none of them will escape. [Towns in] the valleys and on the plateau will [all] be destroyed, because [I, ] Yahweh, have said that is what will happen.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Spread salt on the ground in order that it will become a wasteland with [nothing growing there any more], and no one will be living in it!”
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Yahweh will curse anyone who will not eagerly do what he desires, anyone who refrains from using his sword to kill [MTY] others [in Moab].
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
[The people of] Moab have always felt secure; they have never been (exiled/forced [by their enemies] to go to other countries). They are like [MET] wine that has been left undisturbed [in a container for many days to give it good flavor], so now it smells good, and it tastes good.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
But Yahweh says that there will be a time when he will send [enemies to attack them]; they will get rid of the people of Moab like people pour out wine [on the ground] and then smash the wine jar.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
Then [the people of] Moab will be ashamed of [their god/idol] Chemosh [because it did not help them], like the Israeli people were ashamed because their gold statue of a calf [was smashed] at Bethel.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
[The soldiers of Moab previously] said, “We are warriors; we have fought bravely in battles!”
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
But now our King, who is Yahweh, who is called ‘the Commander of the armies of angels’, says that [the country of] Moab and all the towns in it will be destroyed. Their fine young men will [all] be slaughtered.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
Moab will very soon be destroyed. It will soon experience disaster.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
You [people who live in nations] near Moab, who know that it is very famous, should mourn for Moab, and say, “Its glorious power [MTY, DOU] is [completely] ended/broken.”
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
You people of Dibon [city], stop being proud because of being honored, and sit in the dust/dirt, because those who will destroy other places in Moab will attack your [city] and destroy your high walls.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
You people of Aroer [town], stand along the road and watch. Shout to the men and women who will be fleeing [from Moab], “What has happened [there]?”
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
[They will reply], “Moab is ruined and [we are] disgraced!” [So] weep and wail [DOU]. Proclaim at the Aroer [River] that Moab has been destroyed.
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
[Yahweh] will have punished [the towns in Moab that are on] the (plateau/high level): Holon and Jahaz and Mephaath,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
Dibon and Nebo and Beth-Diblathaim,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
Kiriathaim and Beth-Gamul and Beth-Meon,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
Kerioth and Bozrah, cities that are near [each other] and towns that are far away [from each other].
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
Yahweh says, “The power [MTY] of Moab will be ended; [it is as though] [MET] Moab will have a broken arm.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
[You people of] Moab have rebelled against [me, ] Yahweh; so [now] I will cause you all to [stagger like] [SIM] drunken people. [You people of] will wallow in your own vomit and be ridiculed.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
You [people of Moab] ridiculed [the people of] Israel [RHQ]. You treated them as though they were thieves [RHQ]. You shook your head at them scornfully and despised them [RHQ].
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
You people who live in Moab, you should abandon your towns and go and live in caves. Be like [SIM] doves that make their nests in the entrances of caves.”
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
We have [all] heard that [the people of] are very proud; they are extremely proud and conceited/arrogant. [IDM, DOU]
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
But Yahweh says, “I know about that, but it is useless for them to boast [because] it will accomplish nothing.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
So [now] I will wail for Moab; I will cry about all its people. I will moan for the men of Kir-Hareseth [city], [the old capital of Moab].
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
You people of Sibmah [city], you have many vineyards. [It is as though] the branches of your vines extend across the [Dead] Sea to Jazer [city].
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
But no one will be joyful or happy in Moab now; your fruit and grapes that ripen in the (summer/hot season) will soon be destroyed. There will be no grape juice coming from the winepresses, [so] there will be no wine. People will not shout joyfully as they tread on the grapes; people will shout, but they will not be shouting joyfully.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
Instead, the sound of their wailing will rise from Heshbon [city] to Elealeh [town] and Jahaz [village], from Zoar [city] as far as Horonaim [town] and Eglath-Shelishiyah [village]. Even the water in Nimrim [Stream] will be dried up.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
[I, ] Yahweh, say that I will get rid of the people who offer sacrifices on the hilltops, and burn incense to their gods.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
I [SYN] moan for the people of Moab and Kir-Hareseth like [SIM] [someone playing a funeral song on] a flute, because [all] their wealth will disappear.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
The men will shave their heads and their beards [to show that they are mourning]. They all will slash their hands and wear (rough cloth/sackcloth) around their waists.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
In every home and in the town plazas/centers in Moab there will be [people who are] mourning, because I will have destroyed Moab like [SIM] someone smashes an [old] jar that no one wants [any more].
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Moab will be completely shattered! And you will hear the people wailing loudly! They will be disgraced. Moab will become a nation that people ridicule. The people in nearby [countries] will be horrified [about what has happened there].
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
This is what [I, ] Yahweh, say: ‘Look! Their enemies will be swooping/rushing down over Moab like an eagle [SIM] swoops down [to seize an animal].
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Its cities will be captured, its fortresses will be seized. [Even] their warriors will be [afraid], like [SIM] a woman who is about to give birth.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
[The leaders of] Moab boasted against [me, ] Yahweh, so Moab will be destroyed.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
[I, ] Yahweh, say that you people of Moab will be terrified, and fall into pits and traps.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
Those who are terrified and try to run away will fall into deep pits. Whoever climbs out of a pit will be caught in a trap, because I will punish them at the time that I have chosen.’
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
The people will flee as far as Heshbon [city], but they will not be able to go any further, because a fire will burn in Heshbon, [which is the city] where [King] Sihon lived [long ago], and it will burn up all the people [SYN] in Moab who noisily/loudly boasted very much.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
[You people of] Moab, terrible things will happen to you! You people who worship [your god] Chemosh, you will be destroyed. Your sons and your daughters will be captured and taken away [to other countries].
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
But some day, I will enable the people of Moab to return to their land again. [That will surely happen because I, ] Yahweh, have said it.” That is the end of what I prophesied about Moab.

< Irmiya 48 >