< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
Of Moab. "Thus says the LORD of hosts, the God of Israel: 'Woe to Nebo, because it is about to be destroyed; Kiriathaim will be put to shame, it will be taken captive. The fortress is put to shame and broken down.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
The praise of Moab is no more; in Heshbon they have devised evil against her: "Come, and let us cut her off from being a nation." You also, Madmen, shall be brought to silence: the sword shall pursue you.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
The sound of a cry from Horonaim, "destruction and great calamity."
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Moab is destroyed; her little ones have caused a cry to be heard.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
For by the ascent of Luhith with continual weeping shall they go up; for at the descent of Horonaim they have heard the distress of the cry of destruction.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
"Flee, save your lives, and be like a shrub in the wilderness."
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
For, because you have trusted in your works and in your treasures, you also shall be taken: and Chemosh shall go forth into captivity, his priests and his officials together.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
The destroyer shall come on every city, and no city shall escape; the valley also shall perish, and the plain shall be destroyed; as the LORD has spoken.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Give wings to Moab, that she may fly and get her away: and her cities shall become a desolation, without any to dwell in them.'
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Cursed is he who does the work of the LORD negligently; and cursed is he who keeps back his sword from blood.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
'Moab has been at ease from his youth, and he has settled on his lees, and has not been emptied from vessel to vessel, neither has he gone into captivity: therefore his taste remains in him, and his scent is not changed.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
Therefore look, the days come,' says the LORD, 'that I will send to him those who pour off, and they shall pour him off; and they shall empty his vessels, and break their bottles in pieces.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
Moab shall be ashamed of Chemosh, as the house of Israel was ashamed of Bethel their confidence.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
How can you say, "We are mighty men, and valiant men for the war?"
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
Moab is laid waste, and they are gone up into his cities, and his chosen young men are gone down to the slaughter,' says the King, whose name is the LORD of hosts.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
The calamity of Moab is near to come, and his affliction hurries fast.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
All you who are around him, bemoan him, and all you who know his name; say, "How is the strong staff broken, the beautiful rod."
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
You daughter who dwells in Dibon, come down from your glory, and sit in thirst; for the destroyer of Moab has come up against you, he has destroyed your strongholds.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
Inhabitant of Aroer, stand by the way, and watch: ask him who flees, and her who escapes; say, "What has been done?"
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
"Moab is disappointed; for it is broken down: wail and cry; tell it by the Arnon, that Moab is laid waste."
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
Judgment has come on the plain country, on Holon, and on Jahzah, and on Mephaath,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
and on Dibon, and on Nebo, and on Beth Diblathaim,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
and on Kiriathaim, and on Beth Gamul, and on Beth Meon,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
and on Kerioth, and on Bozrah, and on all the cities of the land of Moab, far or near.
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
The horn of Moab is cut off, and his arm is broken,' says the LORD.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
'Make him drunk; for he magnified himself against the LORD: and Moab shall wallow in his vomit, and he also shall be in derision.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
For wasn't Israel a derision to you? Was he found among thieves? For as often as you speak of him, you shake your head.
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
You inhabitants of Moab, leave the cities, and dwell in the rock; and be like the dove that makes her nest over the mouth of the abyss.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
We have heard of the pride of Moab--he is very proud--of his pride, and his vanity, and his arrogance, and the haughtiness of his heart.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
I know his wrath,' says the LORD, 'that it is nothing; his boastings have worked nothing.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
therefore I will wail for Moab; yes, I will cry out for all Moab; I will mourn for the men of Kir Heres.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
With more than the weeping of Jazer will I weep for you, vine of Sibmah: your branches passed over the sea, they reached even to Jazer; on your summer fruits and on your vintage the destroyer is fallen.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
Gladness and joy is taken away from the fruitful field and from the land of Moab; and I have caused wine to cease from the wine presses: none shall tread with shouting; the shouting shall be no shouting.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
From the cry of Heshbon even to Elealeh, even to Jahaz have they uttered their voice, from Zoar even to Horonaim, to Eglath Shelishiyah: for the waters of Nimrim also shall become desolate.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
And I will cause to cease in Moab,' says the LORD, 'the one who offers sacrifice upon the high place, and the one who burns incense to his gods.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
Therefore my heart sounds for Moab like pipes, and my heart sounds like pipes for the men of Kir Heres: therefore the abundance that he has gotten is perished.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
For every head is bald, and every beard clipped: on all the hands are cuttings, and on the waist sackcloth.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
On all the housetops of Moab and in its streets there is lamentation every where; for I have broken Moab like a vessel in which none delights,' says the LORD.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
How it is broken down. How they wail. How Moab has turned the back with shame. So shall Moab become a derision and a terror to all who are around him.'
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
For thus says the LORD: 'Look, he shall fly as an eagle, and shall spread out his wings against Moab.
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Kerioth is taken, and the strongholds are seized, and the heart of the mighty men of Moab at that day shall be as the heart of a woman in her pangs.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
Moab shall be destroyed from being a people, because he has magnified himself against the LORD.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
Fear, and the pit, and the snare, are on you, inhabitant of Moab, says the LORD.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
He who flees from the fear shall fall into the pit; and he who gets up out of the pit shall be taken in the snare: for I will bring on him, even on Moab, the year of their visitation,' says the LORD.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
'Those who fled stand without strength under the shadow of Heshbon; for a fire has gone forth out of Heshbon, and a flame from the city of Sihon, and it has destroyed the forehead of Moab, and the crown of the sons of tumult.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
Woe to you, O Moab. The people of Chemosh is undone; for your sons are taken away captive, and your daughters into captivity.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
Yet will I bring back the captivity of Moab in the latter days,' says the LORD. Thus far is the judgment of Moab."

< Irmiya 48 >