< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
Against Moab. Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Woe unto Nebo! for it is wasted; made ashamed, captured is Kiryathayim; made ashamed is Misgab and dismayed.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
There is no more praise of Moab: in Cheshbon have they devised evil against it, “Come, and let us cut it off from being a nation.” Also thou Madmen shalt be ruined; after thee shall pursue the sword.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
There is a voice of crying from Choronayim, destruction and a great breach.
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Broken down is Moab: her little ones send forth a cry of distress.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
For the ascent of Luchith is ascended with weeping and tears; for on the descent of Choronayim the enemies have heard the cry of destruction.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
Flee, save your life, and be ye like the solitary tree in the wilderness.
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
For, because thou hast trusted in thy works and in thy treasures, thou also shalt be conquered: and Kemosh shall go forth into exile, [with] his priests and his princes together.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
And the water shall come over every city, and no city shall escape: and lost shall be the valley, and destroyed shall be the plain, as the Lord hath said.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Give wings unto Moab, that she may flee and get away; since her cities shall become desolate, without any to dwell therein.
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Cursed be he that doth the work of the Lord negligently, and cursed be he that withholdeth his sword from blood.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
Moab was ever at ease from his youth, and he was resting on his lees, and was not emptied from vessel to vessel, and had not gone into exile: therefore had his taste remained in him, and his scent was not changed.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
Therefore, behold, days are coming, saith the Lord, when I will send unto him tappers, that shall tap him, and they shall empty his vessels, and dash in pieces their bottles.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
And Moab shall be ashamed of Kemosh, as the house of Israel were made ashamed because of Beth-el their confidence.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
How can ye say, We are mighty and men of bravery for the war?
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
Moab is wasted, and into his cities hath [the enemy] ascended, and his chosen young men are gone down to the slaughter, saith the King, the Lord of hosts is his name.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
Near is the calamity of Moab to come, and his misfortune hasteneth fast.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
All ye that are about him bemoan him; and all ye that know his name: say, How is the strong staff broken, the beautiful stick!
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
Come down from thy glory, and sit in thirst, thou inhabitress, daughter of Dibon; for the waster of Moab cometh up against thee, he destroyeth thy strong-holds.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
Stand by the way, and look out, O inhabitress of 'Aro'er: ask him that fleeth, and her that escapeth, say, What hath been done?
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
Moab hath been made ashamed; for it is broken down; wail, and cry aloud: tell ye it by the Arnon, that Moab is wasted,
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
And punishment is come over the land of the plain, over Cholon, and over Yahzah, and over Mepha'ath,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
And over Dibon, and over Nebo, and over Beth-diblathayim,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
And over Kiryathayim, and over Beth-gamul, and over Beth-me'on,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
And over Keriyoth, and over Bozrah, and over all the cities of the land of Moab, that are far and that are near.
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
Hewn away is the horn of Moab, and his arm is broken, saith the Lord.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
Make him drunken; for he magnified himself against the Lord: and Moab shall wallow in his vomit, and he also shall become [an object] of derision.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
For was not Israel a derision unto thee? or was he found among thieves? that whenever thou spokest of him, thou hadst to shake [thy head]?
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
Leave the cities, and dwell on rocks, O ye that dwell in Moab; and be ye like the dove that maketh her nest in the sides of the mouth of rocky clefts.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
We have heard the pride of Moab, who is so exceedingly proud, his haughtiness, and his pride, and his arrogance, and the overbearingness of his heart.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
I will know, saith the Lord, his wrath, and how causeless it is: his liars have done what is not right.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
Therefore will I wail for Moab, and for all Moab will I cry out; for the men of Kir-cheres shall people moan.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
With the weeping of Ya'zer will I weep for thee, O vine of Sibmah; thy tendrils [once] passed over the sea, they reached as far as to the sea of Ya'zer: over thy summer-fruits and over thy vintage the waster is fallen.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
And banished are joy and gladness from Carmel, and from the land of Moab; and I have caused the wine to cease from the wine-presses; none shall tread the press with the vintner's call; battle cry—nor vintner's call.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
From the loud cry of Cheshbon as far as El'aleh, even unto Yahaz, have they sent forth their voice, from Zo'ar even unto Choronayim, to the third 'Eglath; for the waters also of Nimrim shall become desolate.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
Moreover will I cause to cease unto Moab, saith the Lord, him that offereth on the high-places, and him that burneth incense to his gods.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
Therefore shall my heart groan for Moab like flutes, and my heart shall groan like flutes for the men of Kir-cheres; for the cause that the remnant of the riches he had gotten are lost.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
For every head is bald, and every beard is shorn: upon all the hands are cuttings, and upon the loins is sackcloth.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
Upon all the roofs of Moab, and in her streets, there is everywhere lamentation; for I have broken Moab like a vessel which hath no value, saith the Lord.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Oh, how is it broken down! wail! how hath Moab turned the back with shame! and Moab shall be a derision and a dismay to all those around him.
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
For thus hath said the Lord, Behold, as the eagle shall he fly, and he shall spread out his wings over Moab.
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Captured are the fortresses, and the strong-holds are conquered: and the heart of the mighty men of Moab shall be on that day as the heart of a woman in her pangs.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
And Moab shall be destroyed from being a people; because it hath magnified himself against the Lord.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
Terror, and the pit, and the snare, shall be upon thee, O inhabitant of Moab, saith the Lord.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
He that fleeth from the terror shall fall into the pit; and he that getteth up out of the pit shall be caught in the snare; for I will bring upon it, even upon Moab, the year of their visitation, saith the Lord.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
Under the shadow of Cheshbon stand still, deprived of strength, those that flee; but a fire cometh forth out of Cheshbon, and a flame from the midst of Sichon, and it devoureth the corner of Moab, and the crown of the head of the children of vaunting.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
Woe unto thee, O Moab! lost is the people of Kemosh; for thy sons are taken captives, and thy daughters into captivity.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
Yet will I bring back again the captivity of Moab in the end of days, saith the Lord. Thus far is the punishment of Moab.

< Irmiya 48 >