< Irmiya 48 >
1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
Moab taranlahoi, ransahu BAWIPA Isarel Cathut ni hettelah a dei, Nebo teh yawthoe lah ao. Rawknae koe a pha. Kiriathaim teh yeiraipo lah ao. Pâmit e lah ao. Misgab rapanim teh yeiraipo e hoi raphoe e lah ao.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
Moab min kamthangnae a kahma han. Heshbon a rawk nahan kâcai laihoi tho awh, miphun a coungnae dawk hoi tâkhawng awh sei, telah ati awh. Oe Madmen, nang hai tâtueng e lah na o vaiteh tahloi hoi pâlei e lah na o han.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
Horonaim hoi hramnae kamthang rektapnae hoi rawkphainae kamthang hah!
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Moab teh a kahma toe, a canunaw khuika lawk thai lah ao toe.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
Luhith mon dawk ka laihoi a luen awh teh, Horonaim cathuknae koe rawkphainae kamthang hoi kângairunae hah thai lah ao.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
Yawng awh na hringnae rungngang hanlah kahrawng e la patetlah yawng awh.
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
Thaw na tawknae kutnaw hoi na hnopainaw na kâuepkhai dawkvah nang hai man e lah na o han, Khemosh teh a vaihma hoi kahrawikungnaw hoi san lah man e lah ao han.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
Kho tangkuem dawk karaphoekung a tho vaiteh kho buet touh boehai hlout mahoeh. Tanghling dawk e ramnaw hai he a pâmit han. BAWIPA ni a dei tangcoung e patetlah a yawn hai raphoe lah ao han.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
A kamleng thai nahanlah Moab teh rathei poe awh, bangkongtetpawiteh, a khonaw teh kho ka sak e tami awm laipalah kingdi awh han.
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Pamda laihoi BAWIPA thaw ka tawk e teh thoebo lah awm seh, thipaling lawng hanlah a tahloi ka hno hoeh e tami teh thoebo lah awm seh.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
Moab teh a nawca hoi a nawm, a laheipadin koe pou ao. Hlaam alouke dawk pahoung boihoeh teh, santoung boihoeh. A kamtuinae lahoi pou a tui teh, a mei hai kâthung boihoeh.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
Hatdawkvah, thaihaw! atueng a pha tawmlei toe, ahnimouh rawbawk hanlah tami katha vaiteh, ahnimouh ni na rabawk awh han, telah BAWIPA ni a dei. Ahnie hlaam teh a poum sak vaiteh, rakkâbawng han.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
Isarel imthung ni a kâuep poung awh e Bethel a kayakhai awh e patetlah Moab ni Khemosh a kayakhai han toe.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
Taran tuk hanlah athakaawme taminaw, tarankahawi e taminaw telah bangtelamaw na ti thai.
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
Moab teh a rawk toe, a khopui teh hmaikhu lah a coung toe. A nawsainaw pueng he a rawp awh han, telah siangpahrang a min ransahu BAWIPA ni ati.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
Moab rawkphainae teh a hnai toe, a rucatnae teh karanglah a tho han.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
Nangmouh a tengpam e naw ni ahni ka khai laihoi, a min kapanueknaw ni hai, kalenpounge hoi thakasai poung e sonron teh a kâkhoe toe telah dei awh.
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
Oe nang canu, Dibon dawk kho ka sak e na tawntanae hah kum takhai nateh, tui kahran laihoi tahungh. Bangkongtetpawiteh, Moab ka raphoe e ni na tuk awh vaiteh, na rapanimnaw a raphoe awh.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
Oe Aroer dawk kho ka sak e canu, lam teng kangdout nateh khenhaw! ka yawng e tongpa hoi ka kâhrawk e napui hah pacei nateh, bangtelamaw telah tet haw.
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
Bangkongtetpawiteh, Moab teh yeiraipo e lah ao teh, he a rawp han. Kâhram laihoi khuikap awh haw. Moab teh rawkphai e lah ao telah Arnon lah pâpho awh.
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
Ayawn ram dawk lawkcengnae a pha toe. Holon hoi Jahzah hoi Mephaath,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
Dibon hoi Nebo hoi Bethdiblathaim,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
Kiriathaim hoi Bethgarmul hoi Bethmeon,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
Kirioth hoi Bozrah hoi Moab ram e khonaw pueng ahlanae koe e hoi a hnainae koe e naw pueng hai,
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
Moab e ki teh tâtueng e lah ao teh, a loung hai khoe pouh e lah ao, telah BAWIPA ni a dei.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
BAWIPA e lathueng a kârasang dawkvah ama hah parui sak awh, Moab teh amae palo dawk a kâkaawk vaiteh panuikhai e lah ao han.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
Isarel nang hai panuikhai e lah ao nahoehmaw. Tamru hoi a kambawng boimaw. Bangkongtetpawiteh, ahnie kong na dei karoitawi na lû na saling.
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
Moab dawk kho ka sak e naw khopui hah yawng takhai awh nateh, lungha rahak vah awm awh. Bakhu ni talung kâko dawk tabu a tuk e patetlah awm awh.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
Moab a kâoupnae ka thai, a kâoup tangak doeh. A kârasangnae a kâpholennae hoi a lungpatanae hoi a lungkârasangnae naw hah.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
A lungkhueknae teh banglahai awm hoeh tie hah ka panue teh a kâoupnae ni banghai thokhai hoeh, telah BAWIPA ni a dei.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
Moab e lathueng kâhram han, Moab hanlah ka ka han. Kirhareseth taminaw hai a ka awh han.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
Jazer khuikanae hlak ka patawn lah ka ka awh han. Oe Sibam misurkung, na dawn hah tui totouh a yam teh Jazer talî totouh a pha. Na paw hoi misurpaw ka raphoekung ni he a raphoe han.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
Lunghawinae hoi nawmnae a kahma toe. A paw e hmuen hoi Moab ram thung hoi misur katinnae dawk ka misur a baw toe. Apihai nawmnae hoi na katin awh mahoeh toe. Hramnae pawlawk hai lunghawinae pawlawk mahoeh toe.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
Heshbon hoi Elealeh dawk a hram awh, Jahaz totouh ka lawk a kampaw. Zoar hoi Horonaim totouh, Eglathshelishiyah totouh, Nimrim tui hai kingdi han.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
Hothloilah, Moab hmuenrasang dawk thuengnae hoi a cathut hanlah hmuitui ka sawi e hah ka pout sak han, telah a BAWIPA ni a dei.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
Hat toteh, tamawi patetlah ka lungthin Moab hanlah ao teh, Kirhareseth taminaw hanlah takhawng e pawlawk patetlah ka lungthin hah a cai. Hatdawkvah, karoumcalah ouk a hmu awh e hnonaw teh awm hoeh toe.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
Lûnaw pueng luengpalueng lah ao teh, pâkha muennaw pueng ngaw e lah ao. Kutnaw pueng a e lah ao teh, keng dawk buri kapawn ao.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
Moab imthungnaw dawk lamthungnaw hoi kho takinnaw dawk khuikanae ao. Bangkongtetpawiteh, Moab teh aphu kaawm hoeh e hlaam patetlah a kâbawng toe, telah BAWIPA ni a dei.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Nâtotouh maw a rawk toung, nâtotouh maw a hram awh toung. Moab teh yeiraipo laihoi a kamlang botoung. Hatdawkvah, Moab teh a tengpam e taminaw hanlah panuikhai e hoi takikatho e lah a coung.
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
Bangkongtetpawiteh, BAWIPA ni hettelah a dei, khenhaw! Mataw patetlah kamleng vaiteh, Moab lathueng a rathei a kadai han.
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Kirioth teh la e lah ao vaiteh, a rapanimnaw vaitalahoi he a raphoe. Hatnae hnin dawk Moab tami athakaawmnaw teh camo ka khe tawmlei e napui ka pataw e lungthin patetlah ao han.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
Moab a kahma vaiteh, miphun kuep mahoeh toe. Bangkongtetpawiteh, BAWIPA lathueng a kâoup.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
Takitho e tangkom hoi karapnaw, Oe Moab dawk kaawm e naw nangmae lathueng a pha, telah BAWIPA ni a dei.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
Takinae ka yawng takhai e tami teh tangkom dawk a bo han, tangkom dawk hoi ka tâcawt e tami teh karap dawk a kâman han. Bangkongtetpawiteh, reknae kum hah Moab e lathueng, Moab e lathueng roeroe vah ka pha sak han, telah BAWIPA ni a dei.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
Heshbon tâhlip dawk ka yawng e naw thabaw laihoi a kangdue awh han. Hahoi Heshbon koehoi hmai a tho vaiteh, Sibon taminaw e lathueng a kaman han Kâoupnaw e Moab kho a deng totouh he a kak han.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
Yawthoe e lah na o Oe Moab, Khemosh taminaw a thayoun awh, na capanaw san lah ceikhai teh na canunaw santoung awh han.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
Hatei, a to hmalah, Moab santoungnae teh ka thung han telah, BAWIPA ni a dei. Moab lawkcengnae teh het totouh doeh.