< Irmiya 47 >

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
Dette er Herrens ord som kom til profeten Jeremias om filistrene, før Farao slo Gasa.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
Så sier Herren: Se, vann stiger op fra nord, og det blir til en flommende elv, og det flommer utover landene og alt som i dem er, byene og dem som bor i dem. Menneskene skriker, og alle som bor på jorden, jamrer sig;
3 da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
når hans veldige hesters hovslag drønner, når hans vogner ramler, når hans hjul dundrer, da ser ikke fedrene sig om efter barna, så motfalne er de
4 Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
for den dags skyld som kommer for å ødelegge alle filistrene, for å utrydde for Tyrus og Sidon alle som er undsloppet og kunde hjelpe; for Herren ødelegger filistrene, dem som er blitt igjen fra øen Kaftor.
5 Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
Gasa er blitt skallet, Askalon er blitt målløst, det som er blitt igjen av deres lavland; hvor lenge vil du skjære i ditt kjøtt?
6 “Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
Ve! Du Herrens sverd, hvor lenge vil du være urolig? Far i din skjede, hvil dig og vær stille!
7 Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”
Hvorledes skulde du holde dig rolig, når Herren har gitt dig befaling? Til Askalon og til havets strand, dit har han stevnet det.

< Irmiya 47 >