< Irmiya 47 >

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
La parole de l'Eternel, qui fut [adressée] à Jérémie le Prophète contre les Philistins, avant que Pharaon frappât Gaza.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
Ainsi a dit l'Eternel: voici des eaux qui montent de l'Aquilon; elles seront comme un torrent débordé; elles se déborderont sur la terre, et sur tout ce qui est en elle, sur la ville, et sur ses habitants; les hommes crieront, et tous les habitants du pays hurleront;
3 da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
A cause du bruit éclatant de la corne des pieds de ses puissants chevaux, à cause de l'impétuosité de ses chariots, et à cause du bruit de ses roues; les pères n'ont pas regardé les enfants, tant ils ont eu les mains lâches.
4 Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
A cause du jour qui vient pour ravager tous les Philistins, [et] pour retrancher à Tyr et à Sidon quiconque restera pour les secourir; car l'Eternel s'en va saccager les Philistins, qui sont les restes de l'Ile de Caphtor.
5 Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
Gaza est devenue chauve; Askélon ne dit plus mot avec le reste de leur vallée; jusques à quand feras-tu des incisions sur toi?
6 “Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
Ha! épée de l'Eternel, jusques à quand ne te reposeras-tu point? rentre en ton fourreau, apaise-toi, et te tiens en repos.
7 Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”
Mais comment te reposerais-tu? car l'Eternel lui a donné charge, il l'a assignée contre Askélon, et contre le rivage de la mer.

< Irmiya 47 >