< Irmiya 47 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
The word of Jehovah which came to Jeremiah the prophet concerning the Philistines, before Pharaoh had smitten Gaza.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
Thus saith Jehovah: Behold, waters rise up out of the North, And they shall become an overflowing torrent, And shall overflow the land, and all that is therein, —The city, and them that dwell therein; And the men shall cry aloud, And all the inhabitants of the land shall wail.
3 da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
At the noise of the stamping of the horses, At the rattling of his chariots, And at the rumbling of his wheels, Fathers look not back for their children, For feebleness of hands,
4 Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
Because of the day which cometh, To lay waste all the Philistines, To cut off from Tyre and from Sidon Every helper that remaineth. For Jehovah will lay waste the Philistines, The remnant of the country of Caphtor.
5 Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
Baldness is come upon Gaza, Askelon is in ruins, And the remnant of their valley! How long wilt thou cut thyself?
6 “Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
Ah! sword of Jehovah, How long ere thou wilt be quiet? Retire into thy scabbard, Rest, and be still!
7 Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”
But how canst thou be at rest, Since Jehovah hath given thee a charge against Askelon, And against the coast of the sea? There hath he appointed it.