< Irmiya 47 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
The word of the Lord that came to Jeremiah, the prophet, against the Philistines, before Pharaoh struck Gaza.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
Thus says the Lord: “Behold, waters will rise up from the north, and they will be like an inundating torrent, and they will cover the land and its plenitude, the city and its inhabitants. The men will cry out, and all the inhabitants of the land will wail,
3 da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
before the uproar of a procession of weapons and of his soldiers, before the commotion of his four-horse chariots and the multitude of his wheels. The fathers have not looked back for the sons, because of feebleness of hands,
4 Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
because of the arrival of the day on which all the Philistines will be devastated, and Tyre and Sidon will be destroyed, with all the rest of their helpers. For the Lord has depopulated the Philistines, the remnant of the island of Cappadocia.
5 Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
Baldness has arrived over Gaza. Ashkelon has been silenced, along with the remnant of their valley. And how long will you continue to be cut down?
6 “Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
O sharp sword of the Lord, how long will you be without rest? Enter your sheath; be refreshed and silenced.
7 Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”
But how can it find rest, when the Lord has ordered it against Ashkelon and against its maritime regions, and when a task has been appointed to it there?”