< Irmiya 46 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
Beseda od Gospoda, ki je prišla preroku Jeremiju zoper pogane;
2 Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
zoper Egipt, zoper vojsko faraona Nehota, egiptovskega kralja, ki je bil pri reki Evfratu v Kárkemišu, ki ga je babilonski kralj Nebukadnezar udaril v četrtem letu Jojakíma, Jošíjevega sina, Judovega kralja.
3 “Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
»›Pripravite majhen ščit in ščit ter se približajte boju.
4 Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
Vprezite konje in vstanite, vi konjeniki in postavite se s svojimi čeladami; zgladite sulice in si nadenite oklepe.
5 Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
Zakaj sem jih videl zaprepadene in obrnjene nazaj? In njihovi mogočni so potolčeni in so naglo zbežali in niso gledali nazaj, kajti strah je bil naokoli, ‹ govori Gospod.
6 “Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
›Ne dopusti, da hitri izgine niti da mogočni človek pobegne; opotekali se bodo in padali proti severu, pri reki Evfratu.
7 “Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
Kdo je ta, ki prihaja gor kakor poplava, katerega vode se premikajo kakor reke?‹
8 Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
Egipt se vzdiguje kakor poplava in njegove vode se premikajo kakor reke; in pravi: ›Šel bom gor in pokril zemljo, uničil bom mesto in njegove prebivalce.
9 Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
Pridite gor, vi konji; in besnite, vi bojni vozovi in naj mogočni možje pridejo naprej. Etiopijci in Libijci, ki prijemajo ščit; in Ludéjci, ki prijemajo in napenjajo lok.
10 Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
Kajti to je dan Gospoda Boga nad bojevniki, dan maščevanja, da se lahko maščuje svojim nasprotnikom in meč bo požiral in ta bo nasičen in opijanjen z njihovo krvjo, kajti Gospod Bog nad bojevniki ima klavno daritev v severni deželi, pri reki Evfratu.
11 “Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
Pojdi gor v Gileád in vzemi balzam, oh devica, egiptovska hči. Zaman boš uporabljala mnoga zdravila, kajti ne boš ozdravljena.
12 Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
Narodi so slišali o tvoji sramoti in tvoje vpitje je napolnilo deželo, kajti mogočen človek se je spotaknil zoper mogočnega in oba skupaj sta padla.‹«
13 Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
Beseda, ki jo je Gospod spregovoril preroku Jeremiju, kako bo babilonski kralj Nebukadnezar prišel in udaril egiptovsko deželo.
14 “Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
›Oznanite v Egiptu, razglasite v Migdólu, razglasite v Nofu in v Tahpanhésu, recite: ›Stoj trdno in se pripravi, kajti meč bo požiral okoli tebe.
15 Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
Zakaj so tvoji hrabri možje pometeni proč? Niso obstali, ker jih je Gospod pognal.
16 Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
Mnoge je pripravil, da padejo, da, eden je padel na drugega. Rekli so: ›Vstanimo in ponovno pojdimo k svojemu ljudstvu in k deželi svojega rojstva, proč od zatiralskega meča.‹
17 A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
Tam so vpili: ›Faraon, egiptovski kralj, je samo hrup; zamudil je določeni čas.‹
18 “Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
› Kakor jaz živim, ‹ govori Kralj, čigar ime je Gospod nad bojevniki: ›Zagotovo, kakor je Tabor med gorami in kakor Karmel pri morju, tako bo on prišel.
19 Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
Oh ti hči, prebivajoča v Egiptu, oskrbi se, da greš v ujetništvo, kajti Nof bo opustošen in zapuščen, brez prebivalca.
20 “Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
Egipt je podoben zelo lepi telici, toda uničenje prihaja; to prihaja iz severa.
21 Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
Prav tako so njegovi najeti možje v njegovi sredi podobni pitanim bikcem; kajti obrnjeni so tudi nazaj in skupaj so pobegnili proč; niso obstali, ker je nadnje prišel dan njihove katastrofe in čas njihovega obiskanja.
22 Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
Njihov glas bo šel kakor kača; kajti korakali bodo z vojsko in zoper njega bodo prišli s sekirami kakor drvarji.
23 Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
Posekali bodo njegov gozd, ‹ govori Gospod, ›čeprav ta ne more biti preiskan, ker jih je več kakor kobilic in so brezštevilni.
24 Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
Egiptovska hči bo zbegana; izročena bo v roko severnega ljudstva.‹
25 Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog, pravi: ›Glejte, kaznoval bom množico iz Noja in faraona in Egipt z njihovimi bogovi in njihovimi kralji, celo faraona in vse tiste, ki zaupajo vanj.
26 Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
Izročil jih bom v roko tistih, ki jim strežejo po življenju, v roko babilonskega kralja Nebukadnezarja in v roko njegovih služabnikov. Potem bo ta naseljen kakor v dneh davnine, ‹ govori Gospod.
27 “Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
›Vendar se ne boj, oh moj služabnik Jakob in ne bodi zaprepaden, oh Izrael, kajti glej, rešil te bom od daleč in tvoje seme iz dežele njihovega ujetništva. Jakob se bo vrnil in bo počival in bo sproščen in nihče ga ne bo naredil prestrašenega.
28 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”
Ne boj se, Jakob, moj služabnik, ‹ govori Gospod, ›kajti jaz sem s teboj, kajti naredil bom popoln konec vseh narodov, kamor sem te pognal. Toda iz tebe ne bom naredil popolnega konca, temveč te bom grajal po meri; vendar te ne bom pustil v celoti nekaznovanega.‹«