< Irmiya 46 >

1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
Rijeè Gospodnja koja doðe Jeremiji proroku za narode:
2 Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
Za Misirce, za vojsku Faraona Nehaona cara Misirskoga, koja bijaše na reci Efratu kod Harkemisa, i razbi je Navuhodonosor car Vavilonski èetvrte godine Joakima sina Josijina cara Judina.
3 “Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
Pripravite štite i štitiæe, i idite u boj;
4 Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
Prežite konje, i pojašite, konjici; postavite se sa šljemovima; utrite koplja, oblaèite se u oklope.
5 Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
Zašto ih vidim gdje se poplašiše, vraæaju se natrag, junaci njihovi polomiše se i bježe bez obzira? Strah je otsvuda, govori Gospod.
6 “Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
Da ne uteèe laki, niti se izbavi jaki; da se na sjeveru na brijegu rijeke Efrata spotaknu i padnu.
7 “Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
Ko je to što se diže kao potok, i vode mu se kolebaju kao rijeke?
8 Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
Misir se diže kao potok i njegove se vode kolebaju kao rijeke; i veli: idem, pokriæu zemlju, zatræu grad i one koji žive u njemu.
9 Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
Izlazite, konji, bjesnite, kola; i neka izaðu junaci, Husi i Fudi, koji nose štitove, i Ludeji, koji nose i natežu luk.
10 Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
Jer je ovaj dan Gospodu Gospodu nad vojskama dan osvete, da se osveti neprijateljima svojim; maè æe ih proždrijeti i nasitiæe se i opiæe se krvlju njihovom; jer æe biti žrtva Gospoda Gospoda nad vojskama u zemlji sjevernoj na rijeci Efratu.
11 “Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
Izidi u Galad i uzmi balsama, djevojko kæeri Misirska; zaludu su ti mnogi lijekovi, neæeš se izlijeèiti.
12 Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
Narodi èuše sramotu tvoju, i vike tvoje puna je zemlja, jer se spotièu junak o junaka, te obojica padaju.
13 Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
Rijeè koju reèe Gospod Jeremiji proroku o dolasku Navuhodonosora cara Vavilonskoga da potre zemlju Misirsku:
14 “Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
Javite u Misiru, i oglasite u Migdolu, oglasite i u Nofu i u Tafnesu, i recite: stani i pripravi se, jer maè proždrije što je oko tebe.
15 Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
Zašto se povaljaše junaci tvoji? Ne stoje, jer ih Gospod obara.
16 Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
Èini, te se mnogi spotièu i padaju jedan na drugoga, i govore: ustani da se vratimo k narodu svojemu i na postojbinu svoju ispred maèa nasilnikova.
17 A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
Vièu ondje: Faraon car Misirski propade, proðe mu rok.
18 “Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
Tako da sam ja živ, govori car, kojemu je ime Gospod nad vojskama; kao Tavor meðu gorama i kao Karmil na moru doæi æe.
19 Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
Spremi što ti treba da se seliš, stanovnice, kæeri Misirska; jer æe Nof opustjeti i spaliæe se da neæe niko živjeti u njemu.
20 “Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
Misir je lijepa junica; ali pogibao ide, ide sa sjevera.
21 Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
I najamnici su njegovi usred njega kao teoci ugojeni, ali se i oni obrnuše i pobjegoše, ne ostaše, jer doðe na njih dan nesreæe njihove, vrijeme pohoðenja njihova.
22 Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
Glas æe njihov iæi kao zmijinji, jer oni idu s vojskom i doæi æe sa sjekirama na nj kao oni koji sijeku drva.
23 Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
I oni æe posjeæi šumu njegovu, govori Gospod, ako joj i nema mjere, jer ih je više nego skakavaca i nema im broja.
24 Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
Posrami se kæi Misirska, predana je u ruke narodu sjevernom.
25 Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
Govori Gospod nad vojskama Bog Izrailjev: evo, ja æu pohoditi ljudstvo u Noji, i Faraona i Misir i bogove njegove i careve njegove, Faraona i sve koji se uzdaju u nj.
26 Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
I daæu ih u ruke onima koji traže dušu njihovu, u ruke Navuhodonosoru caru Vavilonskom i u ruke slugama njegovijem; a poslije æe biti naseljen kao prije, govori Gospod.
27 “Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
A ti se ne boj, slugo moj Jakove, i ne plaši se, Izrailju, jer evo ja æu te izbaviti iz daljne zemlje i sjeme tvoje iz zemlje ropstva njegova; i Jakov æe se vratiti i poèivaæe, i biæe miran i niko ga neæe plašiti.
28 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”
Ti se ne boj, slugo moj Jakove, govori Gospod, jer sam ja s tobom; jer æu uèiniti kraj svijem narodima, u koje te prognah, ali tebi neæu uèiniti kraja, nego æu te pokarati s mjerom, a neæu te ostaviti sasvijem bez kara.

< Irmiya 46 >