< Irmiya 46 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
La parole de l’Éternel, qui vint à Jérémie le prophète, touchant les nations.
2 Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
Sur l’Égypte. Touchant l’armée du Pharaon Neco, roi d’Égypte, qui était près du fleuve Euphrate, à Carkemish, laquelle Nebucadretsar, roi de Babylone, battit en la quatrième année de Jehoïakim, fils de Josias, roi de Juda.
3 “Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
Préparez l’écu et le bouclier, et approchez-vous du combat!
4 Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
Attelez les chevaux, et montez, vous, cavaliers, et présentez-vous en casques! Fourbissez les piques, revêtez les cottes de mailles!…
5 Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
Pourquoi les vois-je terrifiés, se retirant en arrière, et [pourquoi] leurs hommes forts sont-ils battus et fuient-ils sans se retourner? L’épouvante de tous côtés, dit l’Éternel.
6 “Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
Que l’homme léger à la course ne fuie pas, et que le fort n’échappe pas! Au nord, près du fleuve Euphrate, ils ont bronché et sont tombés.
7 “Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
Qui est celui-ci qui monte comme le Nil, [et] dont les eaux s’agitent comme les fleuves?
8 Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
C’est l’Égypte qui monte comme le Nil, et, comme les fleuves, ses eaux s’agitent. Et elle dit: Je monterai, je couvrirai le pays, je détruirai la ville et ceux qui y habitent.
9 Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
Montez, chevaux! et précipitez-vous, chars! et que les hommes forts sortent, Cush et Puth, qui manient le bouclier, et ceux de Lud, qui manient [et] bandent l’arc!
10 Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
car ce jour est [le jour] du Seigneur, l’Éternel des armées, un jour de vengeance, pour se venger de ses ennemis. Et l’épée dévorera, et elle sera rassasiée et abondamment abreuvée de leur sang; car il y a un sacrifice au Seigneur, l’Éternel des armées, dans le pays du nord, près du fleuve Euphrate.
11 “Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
Monte à Galaad, et prends du baume, vierge, fille de l’Égypte! En vain tu multiplies les remèdes, il n’y a point de guérison pour toi.
12 Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
Les nations ont entendu ta confusion, et ton cri a rempli la terre; car l’homme fort a trébuché sur l’homme fort, ils sont tombés tous deux ensemble.
13 Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
La parole que l’Éternel dit à Jérémie le prophète, touchant la venue de Nebucadretsar, roi de Babylone, pour frapper le pays d’Égypte:
14 “Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
Annoncez en Égypte, et faites entendre à Migdol, et faites entendre à Noph et à Takhpanès; dites: Tiens ferme et prépare-toi, car l’épée dévore tout autour de toi.
15 Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
Pourquoi tes hommes forts ont-ils été emportés? Ils n’ont pas tenu ferme, car l’Éternel les a renversés.
16 Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
Il multiplie ceux qui bronchent; même un homme est tombé sur son compagnon, et ils ont dit: Lève-toi, retournons vers notre peuple et au pays de notre naissance, de devant l’épée qui ravage.
17 A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
Ils ont crié là: Le Pharaon, roi d’Égypte, n’est qu’un bruit; il a laissé passer le temps!
18 “Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
Je suis vivant, dit le Roi, l’Éternel des armées est son nom: Comme le Thabor entre les montagnes, et comme le Carmel sur la mer, ainsi il viendra!
19 Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
Fais-toi un bagage de transporté, habitante, fille de l’Égypte, car Noph sera une désolation et sera dévastée, de sorte qu’il n’y aura pas d’habitant.
20 “Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
L’Égypte est une très belle génisse: le taon vient, il vient du nord.
21 Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
Et ses mercenaires au milieu d’elle sont comme des veaux à l’engrais; car eux aussi ont tourné le dos, ils se sont enfuis ensemble, ils n’ont pas tenu ferme; car le jour de leur calamité, le temps de leur visitation, est venu sur eux.
22 Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
Sa voix sera comme celle du serpent; car ils viendront en force, et ils viendront contre elle avec des haches, comme ceux qui coupent les arbres.
23 Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
Ils couperont sa forêt, dit l’Éternel, quoiqu’elle soit inexplorable, car ils sont plus nombreux que les sauterelles, et on ne peut les compter.
24 Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
Elle est honteuse, la fille de l’Égypte, elle est livrée en la main du peuple du nord.
25 Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
L’Éternel des armées, le Dieu d’Israël, dit: Voici, je vais punir l’Amon de No, et le Pharaon, et l’Égypte, et ses dieux, et ses rois, le Pharaon et ceux qui se confient en lui;
26 Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
et je les livrerai en la main de ceux qui cherchent leur vie, et en la main de Nebucadretsar, roi de Babylone, et en la main de ses serviteurs; et après cela elle sera habitée comme aux jours d’autrefois, dit l’Éternel.
27 “Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
Et toi, mon serviteur Jacob, ne crains point, et ne t’effraie pas, Israël! car voici, je te sauve d’un [pays] lointain, et ta semence, du pays de leur captivité, et Jacob reviendra et sera tranquille et en repos, et il n’y aura personne qui l’effraie.
28 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”
Toi, mon serviteur Jacob, ne crains point, dit l’Éternel, car je suis avec toi; car je détruirai entièrement toutes les nations où je t’ai chassé, mais je ne te détruirai pas entièrement, et je te corrigerai avec mesure, et je ne te tiendrai point pour innocent.