< Irmiya 46 >
1 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
The word of the Lord, that was maad to Jeremye, the profete, ayens hethene men;
2 Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
to Egipt, ayens the oost of Farao Nechao, kyng of Egipt, that was bisidis the flood Eufrates, in Charchamys, whom Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, smoot, in the fourthe yeer of Joachym, sone of Josie, kyng of Juda.
3 “Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
Make ye redi scheeld and targat, and go ye forth to batel.
4 Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
Ioyne ye horsis, and stie, ye knyytis; stonde ye in helmes, polische ye speris, clothe ye you in haburiowns.
5 Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
What therfor? Y siy hem dredeful, and turnynge the backis, the stronge men of hem slayn; and thei fledden swiftli, and bihelden not; drede was on ech side, seith the Lord.
6 “Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
A swift man schal not fle, and a strong man gesse not hym silf to be saued; at the north, bisidis the flood Eufrates, thei weren ouer comun, and fellen doun.
7 “Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
Who is this, that stieth as a flood, and hise swelewis wexen greet as of floodis?
8 Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
Egipte stiede at the licnesse of a flood, and hise wawis schulen be mouyd as floodis; and it schal seie, Y schal stie, and hile the erthe; Y schal leese the citee, and dwelleris therof.
9 Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
Stie ye on horsis, and make ye ful out ioie in charis; and stronge men, come forth, Ethiopie and Libie, holdynge scheeld, and Lidii, takynge and schetynge arowis.
10 Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
Forsothe that dai of the Lord God of oostis is a dai of veniaunce, that he take veniaunce of hise enemyes; the swerd schal deuoure, and schal be fillid, and schal greetli be fillid with the blood of hem; for whi the slayn sacrifice of the Lord of oostis is in the lond of the north, bisidis the flood Eufrates.
11 “Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
Thou virgyn, the douyter of Egipt, stie in to Galaad, and take medicyn. In veyn thou schalt multiplie medecyns; helthe schal not be to thee.
12 Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
Hethene men herden thi schenschipe, and thi yellyng fillide the erthe; for a strong man hurtlide ayens a strong man, and bothe fellen doun togidere.
13 Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
The word which the Lord spak to Jeremye, the profete, on that that Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, was to comynge, and to smytynge the lond of Egipt.
14 “Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
Telle ye to Egipt, and make ye herd in Magdalo, and sowne it in Memphis, and seie ye in Taphnys, Stonde thou, and make thee redi, for a swerd schal deuoure tho thingis that ben bi thi cumpas.
15 Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
Whi hath thi strong man wexe rotun? He stood not, for the Lord vndurturnede hym.
16 Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
He multipliede falleris, and a man felle doun to his neiybore; and thei schulen seie, Rise ye, and turne we ayen to oure puple, and to the lond of oure birthe, fro the face of swerd of the culuer.
17 A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
Clepe ye the name of Farao, kyng of Egipt; the tyme hath brouyt noise.
18 “Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
Y lyue, seith the kyng, the Lord of oostis is his name; for it schal come as Thabor in hillis, and as Carmele in the see.
19 Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
Thou dwelleresse, the douyter of Egipt, make to thee vessels of passyng ouer; for whi Memfis schal be in to wildirnesse, and schal be forsakun vnhabitable.
20 “Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
Egipt is a schapli cow calf, and fair; a prickere fro the north schal come to it.
21 Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
Also the hirid men therof, that liueden as caluys maad fatte in the myddis therof, ben turned, and fledden togidere, and miyten not stonde; for the dai of sleynge of hem schal come on hem, the tyme of the visityng of hem.
22 Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
The vois of hem schal sowne as of bras, for thei schulen haste with oost, and with axis thei schulen come to it. As men kittynge doun trees thei kittiden doun the forest therof,
23 Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
seith the Lord, which mai not be noumbrid; thei ben multiplied ouer locustis, and no noumbre is in hem.
24 Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
The douytir of Egipt is schent, and bitakun in to the hond of the puple of the north,
25 Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
seide the Lord of oostis, God of Israel. Lo! Y schal visite on the noise of Alisaundre, and on Farao, and on Egipt, and on the goddis therof, and on the kyngis therof, and on hem that tristen in hym.
26 Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
And Y schal yyue hem in to the hondis of men that seken the lijf of hem, and in to the hondis of Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, and in to the hondis of hise seruauntis; and aftir these thingis it schal be enhabitid, as in the formere daies, seith the Lord.
27 “Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
And thou, Jacob, my seruaunt, drede thou not, and Israel, drede thou not; for lo! Y schal make thee saaf fro fer place, and thi seed fro the lond of his caitiftee; and Jacob schal turne ayen, and schal reste, and schal haue prosperite, and noon schal be, that schal make hym aferd.
28 Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”
And Jacob, my seruaunt, nyle thou drede, seith the Lord, for Y am with thee; for Y schal waste alle folkis, to whiche Y castide thee out; but Y schal not waste thee, but Y schal chastise thee in doom, and Y schal not spare thee as innocent.