< Irmiya 45 >
1 Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
This is the word that Jeremiah the prophet told Baruch son of Neriah. This happened when he wrote in a scroll these words at Jeremiah's dictation—this was in the fourth year of Jehoiakim son of Josiah, king of Judah, and he said,
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
“Yahweh, God of Israel, says this to you, Baruch:
3 Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
You have said, 'Woe is me, for Yahweh has added agony to my pain. My groaning has wearied me; I find no rest.'
4 Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
This is what you must say to him: 'Yahweh says this: See, what I built, I am now tearing down. What I planted, I am now pulling up—I will do this throughout all the earth.
5 Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”
But are you hoping for great things for yourself? Do not hope for that. For see, disaster is coming on all humanity—this is Yahweh's declaration—but I am giving you your life as your plunder everywhere you will go.'”