< Irmiya 45 >
1 Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
The word which he spoke Jeremiah the prophet to Baruch [the] son of Neriah when wrote he the words these on a scroll from [the] mouth of Jeremiah in the year fourth of Jehoiakim [the] son of Josiah [the] king of Judah saying.
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
Thus he says Yahweh [the] God of Israel to you O Baruch.
3 Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
You said woe! please to me for he has added Yahweh sorrow to pain my I am weary with groaning my and rest not I have found.
4 Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
Thus - you will say to him thus he says Yahweh here! [that] which I have built I [am] about to tear down and [that] which I have planted I [am] about to pluck up and all the land it.
5 Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”
And you you are seeking for yourself great [things] may not you seek [them] for here I [am] about to bring calamity on all flesh [the] utterance of Yahweh and I will give to you life your to plunder at all the places where you will go there.