< Irmiya 45 >
1 Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
The word which Jeremiah the prophet spake, unto Baruch son of Neriah, —when he had written these words upon a book, from the mouth of Jeremiah, in the fourth year of Jehoiakim son of Josiah, king of Judah saying—
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
Thus, saith Yahweh, God of Israel, Unto thee, O Baruch, —
3 Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
Thou didst say, Surely woe to me! For Yahweh hath added sorrow unto my pain, —I am weary with my moaning, And rest, have I not found!
4 Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
Thus, shalt thou say unto him Thus, saith Yahweh, —Lo! what I had built, I am pulling down, And what I had planted, I am rooting up, —And that is, all the land:
5 Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”
Wouldst, thou, then seek to secure for thyself great things? Do not seek! For behold me! bringing in calamity upon all flesh, Declareth Yahweh, Nevertheless I will give thee thine own life as a spoil, in all places whithersoever thou goest.