< Irmiya 45 >
1 Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
The word which Jeremiah the prophet spake to Baruch, the son of Neriah, after he had written these words in a book from the mouth of Jeremiah, in the fourth year of Jehoiakim, the son of Josiah, the king of Judah, saying: —
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
Thus saith Jehovah, the God of Israel, to thee, O Baruch!
3 Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
Thou sayest, “Woe now to me, for Jehovah hath added grief to my sorrow! I am weary with my sighing, and find no rest.”
4 Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
Thus shalt thou say to him: Thus saith Jehovah: Behold, that which I myself have builded do I break down, and that which I myself have planted do I pluck up, even this whole land;
5 Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”
and seekest thou great things for thyself? Seek them not; for behold, I am about to bring evil upon all flesh, saith Jehovah; but thy life will I give thee, as a prey, in all places whither thou shalt go.