< Irmiya 45 >
1 Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
The word that Jeremiah the prophet has spoken to Baruch son of Neriah, in his writing these words on a scroll from the mouth of Jeremiah, in the fourth year of Jehoiakim son of Josiah king of Judah, saying,
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
“Thus said YHWH, God of Israel, concerning you, O Baruch:
3 Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
You have said, Woe to me, now, for YHWH has added sorrow to my pain, I have been wearied with my sighing, and I have not found rest.
4 Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
Thus you say to him, Thus said YHWH: Behold, that which I have built I am throwing down, and that which I have planted I am plucking up, even the whole land itself.
5 Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”
And you seek for great things—do not seek, for behold, I am bringing calamity on all flesh—a declaration of YHWH—and I have given your life to you for a spoil, in all places to where you go.”