< Irmiya 44 >
1 Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
Communication faite à Jérémie concernant tous les Judéens établis dans le pays d’Egypte établis à Migdol, Tahpanhès, Nof et dans le district de Patros à savoir:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
"Ainsi parle l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël: Vous avez vu tous les désastres que j’ai infligés à Jérusalem et à toutes les villes de Juda; les voilà réduites aujourd’hui en ruines, personne n’y habite,
3 saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
en punition du mal qu’elles ont fait pour me contrarier, en allant encenser, adorer des divinités étrangères que ni elles, ni vous, ni vos ancêtres n’aviez connues.
4 Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
Je vous envoyais tous mes serviteurs, les prophètes, sans trêve ni relâche, pour vous dire: Ne commettez donc pas cette chose abominable que je déteste!
5 Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
Mais ils n’écoutèrent point, ne prêtèrent point l’oreille pour abandonner leur perversité et cesser d’encenser des divinités étrangères.
6 Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
Aussi ma colère et mon indignation se sont déversées et ont consumé les villes de Juda et les rues de Jérusalem, qui sont devenues une ruine et une solitude comme cela se voit aujourd’hui.
7 “To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
Et maintenant, dit l’Eternel, Dieu-Cebaot, Dieu d’Israël: Pourquoi vous attirer à vous-mêmes de grands maux et faire disparaître du sein de Juda hommes, femmes, enfants et nourrissons, sans même vous conserver un simple reste,
8 Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
en m’irritant par l’oeuvre de vos mains, en offrant de l’encens aux dieux étrangers en ce pays d’Egypte, où vous venez séjourner, ce qui aura pour effet d’amener votre ruine et de vous rendre un objet de malédiction et d’opprobre parmi tous les peuples de la terre?
9 Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
Avez-vous donc oublié les méfaits de vos pères, les méfaits des rois de Juda, ceux de leurs femmes, vos propres méfaits et ceux de vos femmes, qui ont été commis dans le pays de Juda et les rues de Jérusalem?
10 Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
On n’est pas encore contrit ni apeuré! Et on ne suit pas ma loi et mes ordonnances que je vous avais exposées à vous et à vos ancêtres!
11 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
C’Est pourquoi, ainsi parle l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël, je vais tourner ma face contre vous pour votre malheur et pour la destruction totale de Juda.
12 Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
Je prendrai les survivants de Juda qui se sont obstinés à se rendre en Egypte pour y séjourner, et c’en sera fini d’eux: ils tomberont dans le pays d’Egypte, victimes du glaive et de la famine; grands et petits, ils mourront par le glaive et la famine et deviendront un objet d’exécration, de stupeur, de malédiction et d’opprobre.
13 Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
Et je sévirai contre ceux qui sont fixés en Egypte comme j’ai sévi contre Jérusalem, par le glaive, par la famine et par la peste.
14 Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
Personne n’échappera et ne sera sauvé des survivants de Juda, venus pour séjourner là, en Egypte. Quant à retourner au pays de Juda, où certains d’entre eux auraient à coeur de revenir pour s’y fixer, non, il n’y aura que quelques hommes isolés qui reviendront."
15 Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
Mais voici ce que répondirent à Jérémie tous ces hommes qui savaient que leurs épouses encensaient des dieux étrangers, toutes les femmes qui étaient présentes en grande foule, ainsi que la population entière établie dans le pays d’Egypte, à Patros:
16 “Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
"La communication que tu nous fais au nom de l’Eternel, nous ne l’accueillons pas de ta part.
17 Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
Mais, au contraire, nous sommes résolus à faire tout ce que nos lèvres ont proféré: brûler de l’encens à la Reine des cieux, répandre des libations en son honneur, comme nous l’avons fait, nous et nos pères, nos rois et nos princes, dans les villes de Juda et les rues de Jérusalem; car alors nous mangions du pain à satiété, nous vivions heureux et ne connaissions pas les revers.
18 Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
Mais du jour où nous avons cessé de brûler de l’encens à la Reine des cieux et de lui offrir des libations, nous avons manqué de tout, et nous avons été décimés par le glaive et par la famine.
19 Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
Et lorsque nous brûlons de l’encens à la Reine des cieux et répandons des libations en son honneur, est-ce donc à l’insu de nos époux que nous lui confectionnons des gâteaux pour la traiter en divinité et que nous lui faisons des libations?"
20 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
Jérémie répliqua au peuple réuni; aux hommes, aux femmes, à toute cette foule qui lui avait tenu tête:
21 “Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
"Précisément, dit-il, cet acte que vous avez commis de brûler de l’encens dans les villes de Juda et les rues de Jérusalem, vous et vos pères, vos rois et vos princes, ainsi que les gens du peuple, l’Eternel s’en est souvenu et il l’a pris à coeur.
22 Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
Aussi l’Eternel n’a-t-il pu patienter davantage à la vue de la perversité de vos oeuvres et des abominations que vous vous permettiez, et votre pays est devenu une ruine, une solitude, un lieu maudit, que personne n’habite, comme on le voit aujourd’hui.
23 Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
C’Est parce que vous avez offert de l’encens, manqué gravement à l’Eternel, refusant d’écouter sa voix et de suivre sa doctrine, ses statuts et ses avertissements, que cette calamité dont vous êtes témoins aujourd’hui vous a atteints."
24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
Jérémie dit encore à tout le peuple ainsi qu’à toutes les femmes: "Ecoutez la parole de l’Eternel, vous tous, Judéens, qui êtes dans le pays d’Egypte:
25 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
Ainsi parle l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël: Vous dites, vous et vos femmes votre bouche parle et vos mains agissentvous dites: Nous voulons accomplir les voeux que nous avons formulés, brûler de l’encens à la Reine des cieux et lui faire des libations; vous entendez remplir vos engagements et accomplir ponctuellement vos voeux.
26 Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
Eh bien! Ecoutez la parole de l’Eternel, vous tous, judéens, qui demeurez dans le pays d’Egypte: Voici, j’en jure par mon grand nom, dit l’Eternel, mon nom ne sera plus prononcé par la bouche d’aucun des hommes dé Juda; nul ne dira dans tout le pays d’Egypte: aussi vrai qu’existe le Dieu Eternel!
27 Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
Je vais agir rapidement à leur égard, pour leur malheur et non pour leur bien: tous les hommes de Juda qui se trouvent dans le pays d’Egypte périront jusqu’au dernier par le glaive et par! a famine.
28 Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
Quelques-uns seulement, échappés au glaive, retourneront du pays d’Egypte au pays de Juda, ce sera un tout petit nombre; et tous les survivants de Juda, venus pour séjourner en Egypte, sauront quelle est la parole qui triomphe, si c’est la mienne ou la leur.
29 “‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
Et voici pour vous le signe, dit l’Eternel, prouvant que je sévirai contre vous en ces lieux, afin que vous sachiez que mes paroles s’accompliront infailliblement contre vous, pour votre malheur.
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”
Voici ce que déclare l’Eternel: Je vais livrer Pharaon Hofra, roi d’Egypte, au pouvoir de ses ennemis et de ceux qui en veulent à sa vie, de même que j’ai livré Sédécias, roi de Juda, au pouvoir de Nabuchodonosor, qui était son ennemi et en voulait à sa vie."