< Irmiya 44 >
1 Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
The word that was maad to Jeremye, and to alle the Jewis, that dwelliden in the lond of Egipt, dwellinge in Magdalo, and in Taphnys, and in Memphis, and in the lond of Phatures,
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
and seide, The Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Ye sien al this yuel, which Y brouyte on Jerusalem, and on alle the citees of Juda; and lo! tho ben forsakun to dai, and no dwellere is in tho;
3 saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
for the malice which thei diden, to terre me to wrathfulnesse, and that thei yeden, and maden sacrifice, and worschipiden alien goddis, whiche thei knewen not, bothe ye, and thei, and youre fadris.
4 Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
And Y sente to you alle my seruauntis profetis; and Y roos bi nyyte, and sente, and seide, Nyle ye do the word of sich abhomynacioun.
5 Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
And thei herden not, nether bowiden doun her eere, that thei schulen be conuertid fro her yuels, and schulden not make sacrifice to alien goddis.
6 Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
And myn indignacioun and my strong veniaunce is wellid togidere, and is kindlid in the citees of Juda, and in the stretis of Jerusalem; and tho ben turned in to wildirnesse, and wastnesse, bi this dai.
7 “To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
And now the Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Whi doon ye this greet yuel ayens youre soulis, that a man of you perische and a womman a litil child and soukynge perische, fro the myddis of Juda, nether ony residue thing be left in you,
8 Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
that terre me to wraththe bi the werkis of youre hondis, in makynge sacrifice to alien goddis in the lond of Egipt, in to which ye entriden, that ye dwelle there, and that ye perische, and be in to cursyng, and in to schenschipe to alle the folkis of erthe?
9 Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
Whether ye han foryete the yuels of youre fadris, and the yuels of the kingis of Juda, and the yuels of her wiues, and youre yuels, and the yuels of youre wyues, whiche thei diden in the lond of Juda, and in the cuntreis of Jerusalem?
10 Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
Thei ben not clensid `til to this dai, and thei dredden not, and thei yeden not in the lawe of the Lord, and in myn heestis, whiche Y yaf bifore you, and bifore youre fadris.
11 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
Therfor the Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Lo! Y schal sette my face in you in to yuel,
12 Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
and Y schal leese al Juda, and Y schal take the remenauntis of Juda, that settiden her faces, to go in to the lond of Egipt, and to dwelle there; and alle schulen be waastid in the lond of Egipt, thei schulen falle doun bi swerd, and schulen be wastid in hungur, fro the leeste `til to the mooste, thei schulen die bi swerd and hungur, and schulen be in to swering, and in to myracle, and in to cursyng, and in to schenschipe.
13 Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
And Y schal visite on the dwelleris of Egipt, as Y visitide on Jerusalem, in swerd, and in hungur, and in pestilence.
14 Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
And noon schal be, that schal ascape, and be residue of the remenauntis of Jewis, that goen to be pilgrimys in the lond of Egipt, and to turne ayen to the lond of Juda, to which thei reisen her soulis, that thei turne ayen, and dwelle there; thei schulen not turne ayen thidir, no but thei that fledden.
15 Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
Forsothe alle men answeriden to Jeremye, and wisten, that her wyues maden sacrifice to alien goddis, and alle wymmen, of whiche a greet multitude stood, and alle the puple of dwelleris in the lond of Egipt, in Fatures, and seiden,
16 “Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
We schulen not here of thee the word which thou spekist to vs in the name of oure Lord God,
17 Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
but we doynge schulen do ech word that schal go out of oure mouth, that we make sacrifice to the queen of heuene, and that we offre to it moist sacrifices, as we diden, and oure fadris, oure kingis, and oure princes, in the citees of Juda, and in the stretis of Jerusalem; and we weren fillid with looues, and it was wel to vs, and we sien noon yuel.
18 Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
But fro that tyme, in which we ceessiden to make sacrifice to the queen of heuene, and to offre to it moist sacrifices, we hadden nede to alle thingis, and we weren wastid bi swerd and hungur.
19 Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
That if we maken sacrifice to the queen of heuene, and offren to it moist sacrifices, whether withouten oure hosebondis we maden to it cakis, to worschipe it, and looues to be offrid?
20 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
And Jeremye seide to al the puple, ayens the men, and ayens the wymmen, and ayens al the puple, that answeriden to hym the word, and he seide,
21 “Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
Whether not the sacrifice which ye sacrifisiden in the citees of Juda, and in the stretis of Jerusalem, ye, and youre fadris, youre kyngis, and youre princes, and the puple of the lond, terriden God to veniaunce? The Lord hadde mynde on these thingis, and it stiede on his herte;
22 Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
and the Lord myyte no more bere, for the malice of youre studies, and for abhomynaciouns whiche ye diden. And youre lond is maad in to desolacioun, and in to wondryng, and in to curs, for no dwellere is, as this dai is.
23 Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
Therfor for ye maden sacrifice to idols, and synneden to the Lord, and herden not the vois of the Lord, and yeden not in the lawe, and in the comandementis, and in the witnessis of hym, therfor these yuels bifellen to you, as this dai is.
24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
Forsothe Jeremye seide to al the puple, and to alle the wymmen, Al Juda, that ben in the lond of Egipt, here ye the word of the Lord.
25 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
The Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, and spekith, Ye and youre wyues spaken with youre mouth, and filliden with youre hondis, and seiden, Make we oure vowis whiche we vowiden, that we make sacrifice to the queen of heuene, and offre to it moist sacrifices; ye filliden youre vowis, and diden tho in werk.
26 Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
Therfor, al Juda, that dwellen in the lond of Egipt, here ye the word of the Lord; Lo! Y swoor in my greet name, seith the Lord, that my name schal no more be clepid bi the mouth of ech man Jew, seiynge, The Lord God lyueth, in al the lond of Egipt.
27 Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
Lo! Y schal wake on hem in to yuel, and not in to good; and alle the men of Juda, that ben in the lond of Egipt, schulen be waastid, bi swerd and hungur, til thei be wastid outerli.
28 Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
And a fewe men that fledden the swerd, schulen turne ayen fro the lond of Egipt in to the lond of Juda; and alle the remenauntis of Juda, of hem that entren in to the lond of Egipt, to dwelle there, schulen wite, whos word schal be fillid, myn ether hern.
29 “‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
And this schal be a signe to you, seith the Lord, that Y schal visite on you in this place, that ye wite, that verili my wordis schulen be fillid ayens you in to yuel.
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”
The Lord seith these thingis, Lo! Y schal bitake Farao, the kyng of Egipt, in to the hond of hise enemyes, and in to the hond of hem that seken his lijf, as Y bitook Sedechie, the kyng of Juda, in to the hond of Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, his enemye, and sekynge his lijf.