< Irmiya 44 >
1 Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
The word which it came to Jeremiah concerning all the Jews who were dwelling in [the] land of Egypt who were dwelling in Migdol and in Tahpanhes and in Memphis and in [the] land of Pathros saying.
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
Thus he says Yahweh of hosts [the] God of Israel you you have seen all the calamity which I brought on Jerusalem and on all [the] cities of Judah and there! they [are] a ruin the day this and there not in them [is] an inhabitant.
3 saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
Because of wickedness their which they did to provoke to anger me by going to make smoke to serve gods other which not they had known them they you and ancestors your.
4 Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
And I sent to you all servants my the prophets rising early and sending saying may not please you do [the] thing of abomination this which I hate.
5 Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
And not they listened and not they inclined ear their to turn away from wickedness their to not to make smoke to gods other.
6 Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
And it poured forth rage my and anger my and it burned in [the] cities of Judah and in [the] streets of Jerusalem and they became a ruin a desolation as the day this.
7 “To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
And therefore thus he says Yahweh [the] God of hosts [the] God of Israel why? [are] you doing harm great to selves your to cut off to yourselves man and woman child and suckling-child from [the] midst of Judah to not to leave for yourselves a remnant.
8 Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
By provoking to anger me by [the] deeds of hands your by making smoke to gods other in [the] land of Egypt where you [have] come to sojourn there so as to cut off to yourselves and so as to become you a curse and a reproach among all [the] nations of the earth.
9 Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
¿ Have you forgotten [the] wicked deeds of ancestors your and [the] wicked deeds of - [the] kings of Judah and [the] wicked deeds of wives his and wicked deeds your and [the] wicked deeds of wives your which they did in [the] land of Judah and in [the] streets of Jerusalem.
10 Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
Not they have been made contrite until the day this and not they have feared and not they have walked in law my and in decrees my which I set before you and before ancestors your.
11 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
Therefore thus he says Yahweh of hosts [the] God of Israel here I [am] about to set face my on you for harm and to cut off all Judah.
12 Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
And I will take away [the] remnant of Judah who they set faces their to go [the] land of Egypt to sojourn there and they will meet their end everyone in [the] land of Egypt they will fall by the sword by famine they will meet their end from [the] small and unto [the] great by the sword and by famine they will die and they will become an curse a horror and a curse and a reproach.
13 Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
And I will visit [judgment] on those [who] dwell in [the] land of Egypt just as I visited [judgment] on Jerusalem by the sword by famine and by pestilence.
14 Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
And not he will belong an escapee and a survivor to [the] remnant of Judah who went to sojourn there in [the] land of Egypt and to return - [the] land of Judah where they [are] lifting up desire their to return to dwell there for not they will return that except fugitives.
15 Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
And they answered Jeremiah all the men who knew that [were] making smoke wives their to gods other and all the women who were standing by a company great and all the people who were dwelling in [the] land of Egypt in Pathros saying.
16 “Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
The word which you have spoken to us in [the] name of Yahweh not we [are] about to listen to you.
17 Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
For certainly we will do every thing - which it has gone out from mouth our to make smoke to [the] queen of the heavens and to pour out to her drink offerings just as we have done we and ancestors our kings our and officials our in [the] cities of Judah and in [the] streets of Jerusalem and we were satisfied food and we were good and distress not we saw.
18 Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
And from then we ceased to make smoke to [the] queen of the heavens and to pour out to her drink offerings we have lacked everything and by the sword and by the famine we have met our end.
19 Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
And if we [were] making smoke to [the] queen of the heavens and to pour out to her drink offerings ¿ without husbands our did we make for her cakes to form image her and to pour out to her drink offerings.
20 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
And he said Jeremiah to all the people to the men and to the women and to all the people who had answered him a word saying.
21 “Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
¿ Not the incense which you made smoke in [the] cities of Judah and in [the] streets of Jerusalem you and ancestors your kings your and officials your and [the] people of the land them did he remember Yahweh and did it come up on heart his.
22 Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
And not he was able Yahweh still to endure because of [the] wickedness of deeds your because of the abominations which you did and it has become land your a desolation and a waste and a curse from not inhabitant as the day this.
23 Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
Because that you made smoke and that you had sinned to Yahweh and not you listened to [the] voice of Yahweh and in law his and in decrees his and in testimonies his not you walked there-fore it has happened to you the calamity this as the day this.
24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
And he said Jeremiah to all the people and to all the women hear [the] word of Yahweh O all Judah which [is] in [the] land of Egypt.
25 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
Thus he says Yahweh of hosts [the] God of Israel saying you and wives your and you have spoken with mouth your and with hands your you have fulfilled - saying certainly we will perform vows our which we have vowed to make smoke to [the] queen of the heavens and to pour out to her drink offerings certainly you will carry out vows your and certainly you will perform vows your.
26 Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
Therefore hear [the] word of Yahweh O all Judah who are dwelling in [the] land of Egypt here I I swear by own name my great he says Yahweh if it will be again name my named - by [the] mouth of - any person of Judah [who] says [by] [the] life of [the] Lord Yahweh in all [the] land of Egypt.
27 Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
Here I [am] watching over them for harm and not for good and they will meet their end every person of Judah who [is] in [the] land of Egypt by the sword and by famine until come to an end they.
28 Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
And escapees of [the] sword they will return! from [the] land of Egypt [the] land of Judah men of number and they will know all [the] remnant of Judah who went to [the] land of Egypt to sojourn there [the] word of whom? will it be established from me and from them.
29 “‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
And this for you [will be] the sign [the] utterance of Yahweh that [am] about to visit [judgment] I on you in the place this so that you may know that certainly they will be established words my on you for harm.
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”
Thus - he says Yahweh here I [am] about to give Pharaoh Hophra [the] king of Egypt in [the] hand of enemies his and in [the] hand of [those who] seek life his just as I gave Zedekiah [the] king of Judah in [the] hand of Nebuchadnezzar [the] king of Babylon enemy his and [one who] sought life his.