< Irmiya 44 >

1 Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
The word that came to Jeremiah for all the Jews who dwell in the land of Egypt, who dwell at Migdol, and at Thachpanches, and at Noph, and in the country of Pathros, saying,
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, You yourselves have seen all the evil that I have brought over Jerusalem, and over all the cities of Judah; and, behold, they are ruins this day, and no man is dwelling in them;
3 saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
Because of their wickedness which they had committed to provoke me to anger, by going to burn incense, to serve other gods, whom they did not know, either they, you, or your fathers.
4 Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
And I sent unto you all my servants the prophets, making them rise early and sending them, saying, Oh, do not commit this abominable thing which I hate.
5 Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
But they hearkened not, and inclined not their ear to turn away from their wickedness, so as not to burn incense unto other gods.
6 Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
Whereupon my fury and my anger were poured forth, and were enkindled in the cities of Judah and in the streets of Jerusalem: and they are become ruins, a desert, as at this day.
7 “To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
And now thus hath said the Lord, the God of hosts, the God of Israel, Wherefore do ye commit so great an evil against your souls, so as to cut off unto you man and woman, child and suckling, out of the midst of Judah, so as not to leave you any remainder,
8 Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
By provoking me unto wrath with the works of your hands, in burning incense unto other gods in the land of Egypt, whither ye are come to sojourn there, in order to cut yourselves off, and in order that ye might become a curse and a disgrace among all the nations of the earth?
9 Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
Have ye forgotten the wickedness of your fathers, and the wickedness of the kings of Judah, and the wickedness of their wives, and your own wickedness, and the wickedness of your wives, which they had committed in the land of Judah, and in the streets of Jerusalem?
10 Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
They are not humbled even up to this day, and they are not afraid, and they walk not in my law, nor in my statutes, that I have set before you and before your fathers.
11 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
Therefore thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Behold, I will set my face against you for evil, and to cut off all Judah.
12 Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
And I will take the remnant of Judah, that have set their faces to go into the land of Egypt to sojourn there, and they shall all come to their end, and in the land of Egypt shall they fall: by the sword [and] by the famine shall they come to their end; from the least even unto the greatest, by the sword and by the famine shall they die; and they shall become an oath, an astonishment, and a curse, and a disgrace.
13 Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
And I will inflict punishment on those that dwell in the land of Egypt, as I have inflicted punishment on Jerusalem, through the sword, through the famine, and through the pestilence:
14 Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
So that there shall be no one that escapeth or remaineth of the remnant of Judah, who are gone into the land of Egypt to sojourn there, that they should return into the land of Judah, to which they direct [the desire of] their soul to return thither to dwell there; for they shall not return, but such as shall escape.
15 Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
Then did all the men who knew that their wives were burning incense unto other gods, and all the women that stood by, a great multitude, and all the people that dwelt in the land of Egypt, in Pathros, answer Jeremiah, saying,
16 “Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
Respecting the word that thou hast spoken unto us in the name of the Lord, we will not hearken unto thee.
17 Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
For to a surety we will do all the word that is gone forth out of our own mouth, to burn incense unto the queen of heaven, and to pour out drink-offerings unto her, as we have done, we, and our fathers, our kings, and our princes, in the cities of Judah, and in the streets of Jerusalem: when we had plenty of food, and fared well, and saw no evil.
18 Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
But since the time we have left off to burn incense to the queen of heaven, and to pour out drink-offerings unto her, have we had a lack of every thing; and we have come to our end through the sword and through the famine.
19 Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
And when we burnt incense to the queen of heaven, and poured out drink-offerings unto her, —was this without [the consent of] our husbands, that we did make cakes for her to make her image, and pour out drink-offerings unto her?
20 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
Then said Jeremiah unto all the people, to the men, and to the women, and to all the people who had answered him [with that] word, saying,
21 “Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
Behold, it was the incense that ye burnt in the cities of Judah, and in the streets of Jerusalem, ye, and your fathers, your kings, and your princes, and the people of the land, which the Lord remembered, and which came into his mind;
22 Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
So that the Lord could no longer endure it, because of the evil of your doings, because of the abominations which ye had committed: therefore is your land become a ruin, and an [object of] astonishment, and a curse, without an inhabitant, as at this day.
23 Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
Because that ye had burnt incense, and because ye had sinned against the Lord, and had not hearkened to the voice of the Lord, and had not walked in his law, in his statutes, and in his testimonies: therefore did this evil befall you, as it is this day.
24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
And Jeremiah said [farther] to all the people, and to all the women, Hear the word of the Lord, all Judah that are in the land of Egypt,
25 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, saying, Ye and your wives have both spoken with your mouth, and fulfilled with your hands, saying, We will surely perform our vows that we have vowed, to burn incense to the queen of heaven, and to pour out drink-offerings unto her: ye will fully accomplish your vows, and fully perform your vows.
26 Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
Therefore hear ye the word of the Lord, all Judah that dwell in the land of Egypt, Behold, I have sworn by my great name, saith the Lord, that my name shall no more be called by the mouth of any man of Judah, saying, “As the Lord Eternal liveth,” in all the land of Egypt.
27 Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
Behold, I will watch over them for evil, and not for good: and all the men of Judah that are in the land of Egypt shall come to their end through the sword and through the famine, until they be destroyed.
28 Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
Yet some that escape the sword shall return out of the land of Egypt into the land of Judah, but few in number; and all the remnant of Judah, that are come into the land of Egypt to sojourn there, shall know whose words shall stand firm, mine, or theirs.
29 “‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
And this shall be unto you the sign, saith the Lord, that I will inflict punishment on you in this place, in order that ye may know that my words shall surely stand firm against you for evil:
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”
Thus hath said the Lord, Behold, I will give Pharaoh-chophra' the king of Egypt into the hand of his enemies, and into the hand of those that seek his life, as I gave Zedekiah the king of Judah into the hand of Nebuchadrezzar the king of Babylon, his enemy, and who had sought his life.

< Irmiya 44 >