< Irmiya 43 >

1 Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa mutane dukan maganar Ubangiji Allahnsu, duk abin da Ubangiji ya aike shi ya faɗa musu,
Or il arriva que, lorsque Jérémie eut achevé toutes ces prophéties, disant au peuple toutes les paroles du Seigneur leur Dieu, paroles pour lesquelles le Seigneur leur Dieu l’avait envoyé vers eux,
2 Azariya ɗan Hoshahiya da Yohanan ɗan Kareya da dukan masu ɗaga kai suka ce wa Irmiya, “Kana ƙarya ne! Ubangiji Allahnmu bai aike ka ka ce, ‘Kada ku tafi Masar don ku zauna a can.’
Azarias, fils d’Osaïas, et Johanan, fils de Carée, et tous les hommes superbes, dirent à Jérémie: Tu parles mensonge, toi; le Seigneur notre Dieu ne t’a pas envoyé, disant: N’entrez point en Egypte afin d’y habiter.
3 Amma Baruk ɗan Neriya yana zuga ka a kanmu don ka ba da mu ga Babiloniyawa, don su kashe mu ko su kai mu zaman bauta a Babilon.”
Mais Baruch, fils de Nérias, t’excite contre nous, afin de nous livrer aux mains des Chaldéens, afin de nous tuer et de nous faire conduire à Babylone.
4 Saboda haka Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da dukan mutane suka yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da su zauna a ƙasar Yahuda.
Et Johanan, fils de Carée, et tous les princes des hommes de guerre et tout le peuple n’écoutèrent pas la voix du Seigneur, afin de demeurer dans la terre de Juda.
5 A maimako, Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe raguwar Yahuda waɗanda suka dawo su zauna a ƙasar Yahuda daga dukan al’umman inda aka kora su.
Mais Johanan, fils de Carée, et tous les princes des hommes de guerre prirent avec eux tous ceux qui étaient restés de Juda, qui étaient revenus de chez toutes les nations dans lesquelles ils avaient été auparavant dispersés, afin d’habiter dans la terre de Juda;
6 Suka kuma kwashe dukan maza, mata da yara da’ya’yan sarki mata waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari tare da Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da Irmiya annabi da kuma Baruk ɗan Neriya.
Les hommes, et les femmes, et les petits enfants, et les filles du roi, et toute âme que Nabuzardan, prince de la milice, avait laissée avec Godolias, fils d’Ahicam, fils de Saphan, et Jérémie le prophète, et Baruch, fils de Nérias;
7 Saboda haka suka shiga Masar cikin rashin biyayya ga Ubangiji suka tafi har can Tafanes.
Et ils entrèrent dans la terre d’Egypte, parce qu’ils n’obéirent pas à la voix du Seigneur; et ils vinrent jusqu’à Taphnis.
8 A Tafanes maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie dans Taphnis, disant:
9 “Yayinda Yahudawa suna kallo, ka ɗauki waɗansu manyan duwatsu tare da kai ka kuma binne su cikin yumɓu a tubalin dakalin ƙofar shiga fadar Fir’auna a Tafanes.
Prends de grandes pierres en ta main, et tu les cacheras dans la voûte qui est sous le mur de brique à la porte de la maison de Pharaon à Taphnis, les hommes de Juda le voyant;
10 Sa’an nan ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, zan aika wa bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon, zan kuma sa kursiyinsa a kan waɗannan duwatsun da na binne a nan; zai fadada bukkar mulkinsa a bisansu.
Et tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur des armées. Dieu d’Israël: Voilà que moi j’enverrai et je prendrai Nabuchodonosor, roi de Babylone, mon serviteur; et je poserai son trône sur ces pierres que j’ai cachées; et il établira son siège sur elles.
11 Zai zo ya yaƙi Masar, ya kawo mutuwa ga waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa, zaman bauta ga waɗanda aka ƙaddara musu zaman bauta, da kuma takobi ga waɗanda aka ƙaddara su mutu ta takobi.
Et venant il frappera la terre d’Egypte: ceux qui sont voués à la mort iront à la mort, et ceux qui le sont à la captivité, à la captivité; et ceux qui le sont au glaive, au glaive.
12 Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
Et il allumera le feu dans les temples des dieux de l’Egypte, et il les brûlera, et il emmènera les dieux captifs; et il se revêtira de la terre de l’Egypte comme un pasteur se revêt de son manteau, et il sortira de là en paix.
13 A can cikin haikalin rana a Masar zai rushe al’amudan duwatsu yă kuma ƙone haikalan allolin Masar.’”
Et il brisera les statues de la maison du soleil qui sont dans la terre d’Egypte; et les temples des dieux de l’Egypte, il les brûlera au feu.

< Irmiya 43 >