< Irmiya 43 >

1 Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa mutane dukan maganar Ubangiji Allahnsu, duk abin da Ubangiji ya aike shi ya faɗa musu,
Or il arriva qu'aussitôt que Jérémie eut achevé de prononcer à tout le peuple toutes les paroles de l'Eternel leur Dieu, pour lesquelles l'Eternel leur Dieu l'avait envoyé vers eux, [savoir] toutes ces choses-là;
2 Azariya ɗan Hoshahiya da Yohanan ɗan Kareya da dukan masu ɗaga kai suka ce wa Irmiya, “Kana ƙarya ne! Ubangiji Allahnmu bai aike ka ka ce, ‘Kada ku tafi Masar don ku zauna a can.’
Hazaria fils de Hosahja, et Johanan fils de Karéah, et tous ces hommes fiers, dirent à Jérémie: tu profères des mensonges; l'Eternel notre Dieu ne t'a pas envoyé nous dire: n'entrez point en Egypte pour y séjourner.
3 Amma Baruk ɗan Neriya yana zuga ka a kanmu don ka ba da mu ga Babiloniyawa, don su kashe mu ko su kai mu zaman bauta a Babilon.”
Mais Baruc fils de Nérija t'incite contre nous, afin de nous livrer entre les mains des Caldéens, pour nous faire mourir, et pour nous faire transporter à Babylone.
4 Saboda haka Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da dukan mutane suka yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da su zauna a ƙasar Yahuda.
Ainsi Johanan fils de Karéah, et tous les Capitaines des gens de guerre, et tout le peuple n'écoutèrent point la voix de l'Eternel, pour demeurer au pays de Juda.
5 A maimako, Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe raguwar Yahuda waɗanda suka dawo su zauna a ƙasar Yahuda daga dukan al’umman inda aka kora su.
Car Johanan fils de Karéah, et tous les Capitaines des gens de guerre prirent tout le résidu de ceux de Juda qui étaient retournés de toutes les nations, parmi lesquelles ils avaient été chassés, pour demeurer dans le pays de Juda;
6 Suka kuma kwashe dukan maza, mata da yara da’ya’yan sarki mata waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari tare da Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da Irmiya annabi da kuma Baruk ɗan Neriya.
Les hommes, et les femmes, et les enfants, et les filles du Roi, et toutes les personnes que Nébuzar-adan prévôt de l'hôtel avait laissées avec Guédalia fils d'Ahikam, fils de Saphan; [ils prirent] aussi Jérémie le Prophète, et Baruc fils de Nérija;
7 Saboda haka suka shiga Masar cikin rashin biyayya ga Ubangiji suka tafi har can Tafanes.
Et ils entrèrent au pays d'Egypte, car ils n'obéirent point à la voix de l'Eternel; et ils vinrent jusqu'à Taphnés.
8 A Tafanes maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Alors la parole de l'Eternel fut [adressée] à Jérémie dans Taphnés, en disant:
9 “Yayinda Yahudawa suna kallo, ka ɗauki waɗansu manyan duwatsu tare da kai ka kuma binne su cikin yumɓu a tubalin dakalin ƙofar shiga fadar Fir’auna a Tafanes.
Prends en ta main de grosses pierres, et les cache dans l'argile, en la tuilerie qui est à l'entrée de la maison de Pharaon à Taphnés, les Juifs le voyant;
10 Sa’an nan ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, zan aika wa bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon, zan kuma sa kursiyinsa a kan waɗannan duwatsun da na binne a nan; zai fadada bukkar mulkinsa a bisansu.
Et leur dis: Ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: voici, je m'en vais mander et faire venir Nébucadnetsar Roi de Babylone mon serviteur, et je mettrai son trône sur ces pierres que j'ai cachées, et il étendra son pavillon sur elles;
11 Zai zo ya yaƙi Masar, ya kawo mutuwa ga waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa, zaman bauta ga waɗanda aka ƙaddara musu zaman bauta, da kuma takobi ga waɗanda aka ƙaddara su mutu ta takobi.
Et il viendra et frappera le pays d'Egypte. Ceux qui [sont destinés] à la mort, [iront] à la mort; et ceux qui [sont destinés] à la captivité, [iront] en captivité; et ceux qui [sont destinés] à l'épée, [seront livrés] à l'épée.
12 Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
Et j'allumerai le feu dans les maisons des dieux d'Egypte, et [Nébucadnetsar] les brûlera, et il emmènera captifs ceux d'Egypte, et il se parera des richesses du pays d'Egypte, comme le pasteur s'enveloppe de son vêtement, et il en sortira en paix.
13 A can cikin haikalin rana a Masar zai rushe al’amudan duwatsu yă kuma ƙone haikalan allolin Masar.’”
Il brisera aussi les statues de la maison du soleil qui est au pays d'Egypte, et brûlera au feu les maisons des dieux d'Egypte.

< Irmiya 43 >