< Irmiya 43 >
1 Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa mutane dukan maganar Ubangiji Allahnsu, duk abin da Ubangiji ya aike shi ya faɗa musu,
It happened that Jeremiah finished proclaiming to all the people all the words of Yahweh their God that Yahweh their God had told him to say.
2 Azariya ɗan Hoshahiya da Yohanan ɗan Kareya da dukan masu ɗaga kai suka ce wa Irmiya, “Kana ƙarya ne! Ubangiji Allahnmu bai aike ka ka ce, ‘Kada ku tafi Masar don ku zauna a can.’
Azariah son of Hoshaiah, Johanan son of Kareah, and all the arrogant men said to Jeremiah, “You are telling lies. Yahweh our God has not sent you to say, 'Do not go to Egypt to live there.'
3 Amma Baruk ɗan Neriya yana zuga ka a kanmu don ka ba da mu ga Babiloniyawa, don su kashe mu ko su kai mu zaman bauta a Babilon.”
For Baruch son of Neriah is inciting you against us to deliver us into the hand of the Chaldeans, for you to cause our death and to make us captives in Babylon.”
4 Saboda haka Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da dukan mutane suka yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da su zauna a ƙasar Yahuda.
So Johanan son of Kareah, all the princes of the army, and all the people refused to listen to Yahweh's voice to live in the land of Judah.
5 A maimako, Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe raguwar Yahuda waɗanda suka dawo su zauna a ƙasar Yahuda daga dukan al’umman inda aka kora su.
Johanan son of Kareah and all the army commanders took away all the remnant of Judah who had returned from all the nations where they had been scattered to live in the land of Judah.
6 Suka kuma kwashe dukan maza, mata da yara da’ya’yan sarki mata waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari tare da Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da Irmiya annabi da kuma Baruk ɗan Neriya.
They took the men and women, the children and the king's daughters, and every person whom Nebuzaradan, the commander of the king's bodyguards, had let remain with Gedaliah son of Ahikam son of Shaphan. They also took Jeremiah the prophet and Baruch son of Neriah.
7 Saboda haka suka shiga Masar cikin rashin biyayya ga Ubangiji suka tafi har can Tafanes.
They went to the land of Egypt, to Tahpanhes, because they did not listen to Yahweh's voice.
8 A Tafanes maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
So the word of Yahweh came to Jeremiah in Tahpanhes, saying,
9 “Yayinda Yahudawa suna kallo, ka ɗauki waɗansu manyan duwatsu tare da kai ka kuma binne su cikin yumɓu a tubalin dakalin ƙofar shiga fadar Fir’auna a Tafanes.
“Take some large stones in your hand, and, in the sight of the people of Judah, hide them in the mortar in the pavement at the entrance to Pharaoh's house in Tahpanhes.”
10 Sa’an nan ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, zan aika wa bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon, zan kuma sa kursiyinsa a kan waɗannan duwatsun da na binne a nan; zai fadada bukkar mulkinsa a bisansu.
Then say to them, “Yahweh of hosts, God of Israel, says this, 'See, I am about to send messengers to take Nebuchadnezzar king of Babylon as my servant. I will place his throne over these stones that you, Jeremiah, have buried. Nebuchadnezzar will place his pavilion over them.
11 Zai zo ya yaƙi Masar, ya kawo mutuwa ga waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa, zaman bauta ga waɗanda aka ƙaddara musu zaman bauta, da kuma takobi ga waɗanda aka ƙaddara su mutu ta takobi.
For he will come and attack the land of Egypt. Anyone who is assigned to death will be given to death. Anyone who is assigned to captivity will be taken captive. Anyone who is assigned to the sword will be given to the sword.
12 Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
Then I will light a fire in the temples of Egypt's gods. Nebuchadnezzar will burn them or capture them. He will clean out the land of Egypt just as shepherds clean vermin off their clothes. He will go out from that place in victory.
13 A can cikin haikalin rana a Masar zai rushe al’amudan duwatsu yă kuma ƙone haikalan allolin Masar.’”
He will break the stone pillars at Heliopolis in the land of Egypt. He will burn the temples of Egypt's gods.'”