< Irmiya 42 >

1 Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
Då trädde fram alle höfvitsmännerna, Johanan, Kareahs son, Jesanja, Hosaja son, samt med allo folkena, både små och stora;
2 Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
Och sade till Propheten Jeremia: Käre, låt våra bön något gälla för dig, och bed för oss Herran din Gud, om alla dessa igenlefda; ty, dess värr! vi äre få igenblefne af mångom, såsom du sjelfver oss ser med din ögon;
3 Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
Att Herren din Gud ville kungöra oss, hvart vi draga, och hvad vi göra skole.
4 Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
Och Propheten Jeremia sade till dem: Nu väl, jag vill höra eder; och si, jag vill bedja Herran edar Gud, såsom I sagt hafven; och allt det Herren eder svarar, det vill jag kungöra eder, och vill intet dölja undan för eder.
5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
Och de sade till Jeremia: Herren vare ett visst och sant vittne emellan oss, om vi icke göre allt det Herren din Gud genom dig oss befallandes varder;
6 Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
Vare sig godt eller ondt, så vilje vi lyda Herrans vår Guds röst, den vi sände dig till; på det oss må väl gå, då vi Herrans vår Guds röst lyde.
7 Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
Efter tio dagar skedde Herrans ord till Jeremia.
8 Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
Då kallade han Johanan, Kareahs son, och alla höfvitsmännerna, som när honom voro, och allt folket, både små och stora;
9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
Och sade till dem: Detta säger Herren, Israels Gud, till hvilken I mig sändt hafven, att jag skulle bära edor bön fram för honom:
10 ‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
Om I blifven i dessa lande, så vill jag uppbygga och icke omkullslå eder; Jag skall plantera och icke upprycka eder; ty det onda, som jag eder gjort hafver, det ångrar mig allaredo.
11 Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
I skolen väl säkre vara för Konungenom i Babel, den I rädens före, säger Herren; I skolen intet frukta honom; ty jag vill vara när eder, att jag skall hjelpa och frälsa eder ifrå hans hand.
12 Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
Jag skall bevisa eder barmhertighet, och förbarma mig öfver eder, och föra eder uti edart land igen.
13 “Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
Men om I sägen: Vi vilje icke blifva i desso landena; på det I ju icke skolen lyda Herrans edars Guds röst;
14 in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
Utan sägen: Nej, vi vilje draga in uti Egypti land, på det vi intet örlig se måge, eller höra basuners ljud, och ingen hunger för bröds brists skull lida, der vilje vi blifva;
15 to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
Nu, så hörer Herrans ord, I qvarblefne af Juda; detta säger Herren Zebaoth, Israels Gud: Om I ställen edor ansigte till att draga in uti Egypten, så att I viljen der blifva;
16 takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
Så skall svärdet, der I frukten eder före, drabba på eder uti Egypti land; och hungren, den I rädens före, skall allestädes följa eder uti Egypten, och skolen der dö.
17 Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
Ty vare sig ho de kunna, som sitt ansigte dit ställa, att de vilja draga in uti Egypten, der till att blifva, de skola dö genom svärd, hunger och pestilentie; och ingen skall qvar blifva, eller undslippa det onda, som jag skall öfver dem komma låta.
18 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
Ty så säger Herren Zebaoth, Israels Gud: Likasom min vrede och grymhet är gången öfver Jerusalems inbyggare, så skall hon ock gå öfver eder, om I dragen in uti Egypten; på det I skolen varda till bannor, till under, till svärjande, och till skam, och aldrig mer få se detta rummet.
19 “Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
Herrans ord gäller eder till, I qvarblefne af Juda, att I icke dragen in uti Egypten; derföre veter, att jag i dag betygar eder;
20 cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
Eljest sen I edra själar illa före; ty I sänden mig till Herran edar Gud, och saden: Bed Herran vår Gud för oss; och allt det Herren vår Gud sägandes varder, det kungör oss, så vilje vi göra derefter.
21 Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
Det hafver jag nu i dag låtit eder få veta; men I hafven intet velat höra Herrans edars Guds röst, eller allt det han mig till eder befallt hafver.
22 Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”
Så skolen I nu veta, att I genom svärd, hunger och pestilentie, dö måsten, uti det rum, dit I akten att draga, att I der bo skolen.

< Irmiya 42 >