< Irmiya 42 >

1 Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
Da kom alle hærførerne, både Johanan, Kareahs sønn, og Jesanja, Hosajas sønn, og alt folket, både små og store,
2 Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
og de sa til profeten Jeremias: La oss bære frem vår ydmyke bønn for dig og bed for oss til Herren din Gud for hele denne rest av folket - for bare nogen få er vi igjen av de mange, således som du selv ser oss her -
3 Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
at Herren din Gud vil la oss få vite hvilken vei vi skal gå, og hvad vi skal gjøre.
4 Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
Profeten Jeremias sa til dem: Jeg skal gjøre det; jeg vil bede til Herren eders Gud efter eders ord, og hvert et ord Herren svarer eder, skal jeg forkynne eder; jeg skal ikke holde et eneste ord skjult for eder.
5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
Da sa de til Jeremias: Herren være et sant og trofast vidne imot oss, dersom vi ikke gjør efter hvert ord som Herren din Gud sender dig til oss med!
6 Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
Enten det er godt eller ondt, vil vi lyde Herrens, vår Guds røst, som vi sender dig til, forat det må gå oss vel, når vi lyder Herrens, vår Guds røst.
7 Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
Ti dager efter kom Herrens ord til Jeremias.
8 Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
Og han kalte til sig Johanan, Kareahs sønn, og alle hærførerne som var med ham, og alt folket, både små og store,
9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
og han sa til dem: Så sier Herren, Israels Gud, som I sendte mig til for å bære frem eders ydmyke bønn for hans åsyn:
10 ‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
Dersom I blir i dette land, så vil jeg bygge eder op og ikke bryte eder ned, plante eder og ikke rykke eder op; for jeg angrer det onde jeg har gjort eder.
11 Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
Frykt ikke for Babels konge, som I nu frykter for, frykt ikke for ham, sier Herren; for jeg er med eder og vil frelse eder og fri eder av hans hånd.
12 Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
Og jeg vil la eder finne barmhjertighet, og han skal forbarme sig over eder og la eder vende tilbake til eders land.
13 “Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
Men dersom I sier: Vi vil ikke bli i dette land, og I ikke lyder Herrens, eders Guds røst,
14 in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
men sier: Nei, vi vil gå til Egyptens land, så vi kan slippe å se krig og høre basunens lyd og hungre efter brød, og der vil vi bli,
15 to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
så hør nu derfor Herrens ord, I som er blitt igjen av Juda: Så sier Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud: Dersom I setter eder fore å dra til Egypten, og I drar dit for å bo der,
16 takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
da skal sverdet I frykter for, nå eder der i Egyptens land, og hungeren som I er redde for, skal følge eder i hælene der i Egypten, og der skal I dø.
17 Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
Og alle de menn som har satt sig fore å dra til Egypten for å bo der, de skal dø ved sverd, hunger og pest, og ingen av dem skal bli igjen og slippe fra den ulykke som jeg lar komme over dem.
18 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
For så sier Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud: Likesom min vrede og harme blev utøst over Jerusalems innbyggere, således skal min harme bli utøst over eder når I kommer til Egypten, og I skal bli til en ed og til en forferdelse og en forbannelse og til spott, og I skal ikke mere se dette sted.
19 “Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
Herren har talt til eder, I som er blitt igjen av Juda: Dra ikke til Egypten! I skal vite at jeg har advart eder idag.
20 cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
For I farer vill og forspiller eders liv; I har jo selv sendt mig til Herren eders Gud og sagt: Bed for oss til Herren vår Gud og forkynn oss alt det Herren vår Gud sier, og vi vil gjøre det.
21 Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
Og jeg har forkynt eder det idag; men I har ikke hørt på Herrens, eders Guds røst, og på alt det som han sendte mig til eder med.
22 Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”
Så skal I nu vite at I skal dø ved sverd, hunger og pest på det sted som I stunder efter å komme til for å bo der.

< Irmiya 42 >