< Irmiya 42 >

1 Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
Tad visi kara virsnieki, Jehohanans, Kareūs dēls, un Jaazanija, Ozajas dēls, un visi ļaudis, mazi un lieli, piegāja
2 Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
Un sacīja uz pravieti Jeremiju: lai jel mūsu sirsnīgā lūgšana tev ir pieņēmīga, un lūdz mūsu dēļ To Kungu, savu Dievu, par šiem atlikušiem, jo no daudziem mēs mazums esam atlikušies, kā tavas acis mūs redz,
3 Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
Ka Tas Kungs, tavs Dievs, mums darītu zināmu to ceļu, pa ko mums jāstaigā un to vārdu, pēc kā mums jādara!
4 Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
Un pravietis Jeremija uz tiem sacīja: es paklausīšu, redzi, es pielūgšu To Kungu, jūsu Dievu, pēc jūsu vārdiem, un visu, ko Tas Kungs atbildēs, to es jums sacīšu un nekā neslēpšu.
5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
Tad tie sacīja uz Jeremiju: lai Tas Kungs pret mums ir patiesīgs un taisns liecinieks, ja mēs nedarīsim pēc ikkatra vārda, ko Tas Kungs, tavs Dievs, mums pavēlēs.
6 Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
Lai būtu labs, lai ļauns, mēs klausīsim Tā Kunga, sava Dieva balsij, pie kā mēs tevi sūtam; lai mums labi klājās, kad mēs Tā Kunga, sava Dieva, balsij klausīsim.
7 Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
Un pēc desmit dienām Tā Kunga vārds notika uz Jeremiju.
8 Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
Tad viņš aicināja Jehohananu, Kareūs dēlu, un visus kara virsniekus, kas bija pie viņa, un visus ļaudis, mazus un lielus.
9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
Un viņš uz tiem sacīja: tā saka Tas Kungs, Israēla Dievs, pie kā jūs mani esat sūtījuši, jūsu lūgšanu nest priekš Viņa vaiga.
10 ‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
Ja jūs paliksiet dzīvot šai zemē, tad Es jūs gribu uztaisīt un nenolauzīt, Es jūs gribu dēstīt un neizraut, jo Man jau ir žēl tā ļaunuma, ko Es jums esmu darījis.
11 Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
Nebīstaties no Bābeles ķēniņa, no kā vaiga jūs bīstaties; nebīstaties no viņa, saka Tas Kungs; jo Es esmu ar jums, jūs atpestīt un jūs izglābt no viņa rokas.
12 Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
Un Es jums došu žēlastību, ka viņš par jums apžēlojās un jūs atkal atlaiž uz jūsu zemi.
13 “Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
Bet ja jūs sacīsiet: mēs šai zemē negribam palikt, un neklausīsiet Tā Kunga, sava Dieva, balsij,
14 in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
Un sacīsiet: Nē, bet mēs iesim uz Ēģiptes zemi, kur neredzēsim karu un nedzirdēsim trumetes balsi, nedz būsim izsalkuši pēc maizes, un tur mēs gribam dzīvot,
15 to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
Nu tad klausiet Tā Kunga vārdu, jūs atlikušie no Jūda! Tā saka Tas Kungs Cebaot, Israēla Dievs: ja jūs savu vaigu griezīsiet, iet uz Ēģipti un iesiet tur piemājot, -
16 takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
Tad tas zobens, no kā jūs bīstaties, jūs panāks Ēģiptes zemē, un tas bads, par ko jūs bēdājaties, jums tur noies pakaļ, un jūs tur nomirsiet.
17 Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
Tā visiem vīriem, kas savu vaigu griež, iet uz Ēģipti, tur piemājot, būs mirt caur zobenu un caur badu un caur mēri, un no tiem neviens neatliks un neizbēgs no tā ļaunuma, ko Es pār tiem vedīšu.
18 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
Jo tā saka Tas Kungs Cebaot, Israēla Dievs: tā kā Mana dusmība un Mana bardzība ir izgāzta pār Jeruzālemes iedzīvotājiem, tā Mana bardzība pār jums izgāzīsies, kad jūs iesiet uz Ēģipti, un jūs būsiet par lāstu un briesmām un par apsmieklu un kaunu, un vairs neredzēsiet šo vietu.
19 “Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
Tas Kungs pret jums runājis, jūs atlikušie no Jūda: neejat uz Ēģipti. Ziniet zinādami, ka es šodien pret jums esmu liecību devis.
20 cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
Jo jūs pieviļat savas dvēseles: Jūs mani esat sūtījuši pie Tā Kunga, sava Dieva, un sacījuši: lūdz par mums To Kungu, mūsu Dievu, un tā kā Tas Kungs, mūsu Dievs, sacīs, tā mums to dari zināmu, un mēs to gribam darīt.
21 Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
Nu es jums to esmu sacījis, bet jūs neklausāt Tā Kunga, sava Dieva, balsij, nedz tam, ar ko Viņš mani pie jums sūtījis.
22 Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”
Tad ziniet nu, ka jūs caur zobenu, caur badu un caur mēri mirsiet tai vietā, kurp gribat iet, tur piemājot.

< Irmiya 42 >