< Irmiya 42 >

1 Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
Alors tous les chefs des troupes, Jochanan, fils de Karéach, Jézania, fils d'Hoshaïa, et tout le peuple, depuis le plus petit jusqu'au plus grand, s'approchèrent,
2 Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
et dirent à Jérémie, le prophète: « Laisse, je te prie, notre supplication être présentée devant toi, et prie pour nous Yahvé ton Dieu, même pour tout ce reste, car nous ne sommes plus qu'un petit nombre parmi beaucoup, comme tes yeux le voient,
3 Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
afin que Yahvé ton Dieu nous montre le chemin que nous devons suivre et les choses que nous devons faire. »
4 Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
Alors Jérémie, le prophète, leur dit: « Je vous ai entendus. Voici, je vais prier Yahvé votre Dieu selon vos paroles, et il arrivera que tout ce que Yahvé vous répondra, je vous l'annoncerai. Je ne vous cacherai rien. »
5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
Et ils dirent à Jérémie: « Que Yahvé soit au milieu de nous un témoin vrai et fidèle, si nous n'agissons pas selon toute la parole que Yahvé, ton Dieu, t'envoie nous dire.
6 Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
Qu'elle soit bonne ou qu'elle soit mauvaise, nous obéirons à la voix de l'Éternel, notre Dieu, vers qui nous t'envoyons, afin que tout aille bien pour nous, quand nous obéissons à la voix de l'Éternel, notre Dieu. »
7 Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
Dix jours après, la parole de Yahvé fut adressée à Jérémie.
8 Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
Il appela Johanan, fils de Karéa, tous les chefs de troupes qui étaient avec lui, et tout le peuple, depuis le plus petit jusqu'au plus grand,
9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
et leur dit: « Yahvé, le Dieu d'Israël, à qui tu m'as envoyé présenter tes supplications devant lui, dit:
10 ‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
Si vous vivez encore dans ce pays, je vous bâtirai et ne vous abattrai pas, je vous planterai et ne vous arracherai pas, car je m'afflige de la détresse que je vous ai causée.
11 Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
Ne craignez pas le roi de Babylone, dont vous avez peur. N'aie pas peur de lui, dit Yahvé, car je suis avec toi pour te sauver et te délivrer de sa main.
12 Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
Je te ferai grâce, afin qu'il ait pitié de toi et que tu retournes dans ton pays.
13 “Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
« Mais si vous dites: Nous n'habiterons pas dans ce pays, et que vous n'obéissez pas à la voix de Yahvé votre Dieu,
14 in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
en disant: Non, mais nous irons au pays d'Égypte, où nous ne verrons pas la guerre, où nous n'entendrons pas le son de la trompette, où nous n'aurons pas faim de pain, et c'est là que nous habiterons »
15 to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
écoutez donc la parole de Yahvé, reste de Juda! Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Si vous vous décidez à entrer en Égypte et à y vivre,
16 takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
l'épée que vous craignez vous atteindra dans le pays d'Égypte, et la famine que vous redoutez vous suivra de près dans ce pays, et vous y mourrez.
17 Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
Il en sera de même pour tous les hommes qui auront pris le parti d'entrer en Égypte pour y vivre. Ils mourront par l'épée, par la famine et par la peste. Aucun d'eux ne restera ou n'échappera au malheur que je ferai venir sur eux'.
18 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
Car Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « De même que ma colère et ma fureur se sont déversées sur les habitants de Jérusalem, de même ma fureur se déversera sur vous, quand vous entrerez en Égypte; vous serez un objet d'horreur, d'étonnement, de malédiction et d'opprobre, et vous ne verrez plus ce lieu.
19 “Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
« Yahvé a parlé à votre sujet, reste de Juda: « N'allez pas en Égypte! ». Sachez bien que je vous ai rendu aujourd'hui ce témoignage.
20 cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
Car vous avez agi de façon trompeuse contre vos propres âmes; vous m'avez envoyé vers l'Éternel, votre Dieu, en disant: Priez pour nous l'Éternel, notre Dieu; et, selon tout ce que dit l'Éternel, notre Dieu, déclarez-le-nous, et nous le ferons.
21 Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
Je vous l'ai annoncé aujourd'hui, mais vous n'avez pas écouté la voix de l'Éternel, votre Dieu, dans tout ce pour quoi il m'a envoyé vers vous.
22 Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”
Maintenant, sachez donc avec certitude que vous mourrez par l'épée, par la famine et par la peste dans le lieu où vous voulez aller vivre. »

< Irmiya 42 >