< Irmiya 42 >
1 Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
And alle the princes of werriours neiyiden, and Johannan, the sone of Caree, and Jeconye, the sone of Josie, and the residue comyn puple, fro a litil man `til to a greet man.
2 Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
And thei seiden to Jeremye, the profete, Oure preier falle in thi siyt, and preie thou for vs to thi Lord God, for alle these remenauntis; for we ben left a fewe of manye, as thin iyen biholden vs; and thi Lord God telle to vs the weie,
3 Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
bi which we schulen go, and the word which we schulen do.
4 Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
Forsothe Jeremye, the profete, seide to hem, Y haue herd; lo! Y preye to oure Lord God, bi youre wordis; Y schal schewe to you ech word, what euere word the Lord schal answere to me, nether Y schal hide ony thing fro you.
5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
And thei seiden to Jeremye, The Lord be witnesse of treuthe and of feith bitwixe vs; if not bi ech word, in which thi Lord God schal sende thee to vs, so we schulen do, whether it be good ether yuel.
6 Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
We schulen obeie to the vois of oure Lord God, to whom we senden thee, that it be wel to vs, whanne we han herd the vois of oure Lord God.
7 Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
Forsothe whanne ten daies weren fillid, the word of the Lord was maad to Jeremye.
8 Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
And he clepide Johannan, the sone of Caree, and alle the princes of werriours, that weren with hym, and al the puple fro the leste `til to the mooste; and he seide to hem,
9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
The Lord God of Israel seith these thingis, to whom ye senten me, that Y schulde mekeli sette forth youre preyeris in his siyt.
10 ‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
If ye resten, and dwellen in this lond, Y schal bilde you, and Y schal not distrie; Y schal plaunte, and Y schal not drawe out; for now Y am plesid on the yuel which Y dide to you.
11 Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
Nyle ye drede of the face of the kyng of Babiloyne, whom ye `that ben ferdful, dreden; nyle ye drede hym, seith the Lord, for Y am with you, to make you saaf, and to delyuere fro his hond.
12 Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
And Y schal yyue mercies to you, and Y schal haue merci on you, and Y schal make you dwelle in youre lond.
13 “Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
Forsothe if ye seien, We schulen not dwelle in this lond, nether we schulen here the vois of oure Lord God, and seie,
14 in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
Nai, but we schulen go to the lond of Egipt, where we schulen not se batel, and schulen not here the noise of trumpe, and we schulen not suffre hungur, and there we schulen dwelle;
15 to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
for this thing, ye remenauntis of Juda, here now the word of the Lord. The Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, If ye setten youre face, for to entre in to Egipt, and if ye entren,
16 takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
to dwelle there, the swerd whiche ye dreden schal take you there in the lond of Egipt, and the hungur for which ye ben angwischid schal cleue to you in Egipt; and there ye schulen die.
17 Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
And alle the men that settiden her face, to entre in to Egipt, and to dwelle there, schulen die bi swerd, and hungur, and pestilence; no man of hem schal dwelle stille, nether schal aschape fro the face of yuel, which Y schal brynge on hem.
18 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
For why the Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, As my strong veniaunce and myn indignacioun is wellid togidere on the dwelleris of Jerusalem, so myn indignacioun schal be wellid togidere on you, whanne ye han entrid in to Egipt; and ye schulen be in to sweryng, and in to wondring, and in to cursyng, and in to schenschipe; and ye schulen no more se this place.
19 “Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
The word of the Lord is on you, ye remenauntis of Juda; nyle ye entre in to Egipt; ye witinge schulen wite, that Y haue witnessid to you to dai;
20 cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
for ye han disseyued youre soulis, for ye senten me to youre Lord God, and seiden, Preye thou for vs to oure Lord God, and bi alle thingis what euer thingis oure Lord schal seie to thee, so telle thou to vs, and we schulen do.
21 Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
And Y telde to you to dai, and ye herden not the vois of youre Lord God, on alle thingis for whiche he sente me to you.
22 Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”
Now therfor ye witynge schulen wite, for ye schulen die bi swerd, and hungur, and pestilence, in the place to which ye wolden entre, to dwelle there.