< Irmiya 42 >

1 Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
Then drew near all the captains of the forces, and Johanan son of Kareah and Jezaniah son of Hoshaiah, —and all the people from the least even unto the greatest;
2 Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
and said unto Jeremiah the prophet—Let our supplication we beseech thee fall prostrate before thee, and pray thou in our behalf unto Yahweh thy God, in behalf of all this remnant, —for we are left a few out of many, just as thine own eyes do behold us:
3 Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
that Yahweh thy God may tell us the way wherein we should walk, —and the thing that we should do.
4 Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
And Jeremiah the prophet, said unto them, I have heard; behold me! praying unto Yahweh your God according to your words, —and it shall come to pass that the whole thing that Yahweh shall answer you, I will tell you, I will keep back from you, nothing.
5 Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
They, therefore said unto Jeremiah, Yahweh be against us, as a witness true and faithful, —if according to all the word which Yahweh thy God shall send thee unto us, so we do not perform:
6 Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
whether for good or for ill, unto the voice of Yahweh our God for which we are sending thee unto him, will we hearken, —to the end it may be well with us, because we will hearken unto the voice of Yahweh our God.
7 Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
And it came to pass at the end of ten days, that the word of Yahweh came unto Jeremiah.
8 Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
Then called he for Johanan son of Kareah, and for all the princes of the forces who were with him—and for all the people from the least even unto the greatest;
9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
and said unto them, Thus, saith Yahweh, God of Israel—unto whom ye sent me, to cause your supplication to fall prostrate before him: —
10 ‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
If ye will indeed abide, in this land, then will I build you up, and not pull [you] down, and plant you and not uproot [you], —for I have compassion as touching the calamity which I have caused you.
11 Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
Do not fear the face of the king of Babylon, of whose face ye are afraid, —do not fear him, Urgeth Yahweh, for with you, am I, to save you, and to deliver you out of his hand:
12 Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
that I may grant you compassions and he may have compassion upon you, —and suffer you to return unto your own soil.
13 “Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
But, since ye are saying, —We will not dwell in this land, —nor hearken unto the voice of Yahweh your God:
14 in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
saying, —No! for, into the land of Egypt, will we go, where we shall not see war, nor the sound of a horn, shall we hear, —nor for bread, shall we be famished, —there, then will we dwell
15 to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
Now, therefore, for this cause, hear ye the word of Yahweh, O remnant of Judah, —Thus! saith Yahweh of hosts, God of Israel, —If, ye do indeed set your faces to enter Egypt and do enter to sojourn there,
16 takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
then shall it come to pass that the sword which ye are fearing shall, there, overtake you, in the land of Egypt, —and the famine which ye are dreading, shall, there, lay fast hold of you, in Egypt, and, there, shall ye die.
17 Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
So shall it be with all the men who have set their faces to enter Egypt to sojourn there, they shall die by sword, by famine or by pestilence, —and they shall have neither survival nor escape, from the face of the calamity which I am about to bring in upon them.
18 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
For—Thus, saith Yahweh of hosts, God of Israel, —Just as mine anger and mine indignation have been poured out upon the inhabitants of Jerusalem, so shall mine indignation be poured out upon you when ye enter into Egypt, —thus shall ye become a curse, and an astonishment and a contempt and a reproach, and ye shall no more see this place.
19 “Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
Yahweh hath spoken concerning you, O ye remnant of Judah, Do not enter into Egypt: Know certainly, that I have taken you to witness to-day.
20 cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
For ye have deceived yourselves at the cost of your lives, for, ye yourselves, sent me unto Yahweh your God, saying, —Pray thou in our behalf, unto Yahweh our God, —and according to all that Yahweh our God shall say, so, tell us and we will do it.
21 Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
Therefore have I told you to-day, —and yet ye have not hearkened unto the voice of Yahweh your God, even in any thing for which he hath sent me unto you.
22 Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”
Now, therefore, know ye certainly, that by sword, by famine, or by pestilence, shall ye die, —in the place whither ye have desired to go, to sojourn.

< Irmiya 42 >