< Irmiya 41 >

1 A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
Et il arriva dans le septième mois qu’Ismahel, fils de Nathanias, fils d’Elisama, de la race royale, et les grands du roi, et dix hommes avec lui vinrent vers Godolias, fils d’Ahicam, à Masphath; et ils mangèrent là des pains ensemble à Masphath.
2 sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
Or Ismahel, fils de Nathanias, se leva, et les dix hommes qui étaient avec lui, et ils frappèrent Godolias, fils d’Ahicam, fils de Saphan, par le glaive, et tuèrent celui qu’avait préposé le roi de Babylone sur la terre.
3 Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
Tous les Juifs aussi qui étaient avec Godolias, à Masphath, et les Chaldéens qui se trouvèrent là, et les hommes de guerre, Ismahel les frappa.
4 Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
Mais le second jour après qu’il eut tué Godolias, personne encore ne le sachant,
5 sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
Quatre-vingts hommes vinrent de Sichem, de Silo et de Samarie, la barbe rasée, et les habits déchirés, et le visage défiguré; ils portaient de l’encens et des présents, afin de les offrir dans la maison du Seigneur.
6 Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
Ismahel, fils de Nathanias, étant donc sorti de Masphath à leur rencontre, allait marchant en pleurant; or, lorsqu’il les eut rencontrés, il leur dit: Venez vers Godolias, fils d’Ahicam,
7 Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
Et lorsqu’ils furent arrivés au milieu de la cité, Ismahel, fils de Nathanias, les tua et les jeta vers le milieu de la fosse, et les hommes qui étaient avec lui.
8 Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
Mais dix hommes se trouvèrent parmi eux qui dirent à Ismahel: Ne nous faites pas mourir, parce que nous avons des trésors cachés dans le champ, du blé, de l’orge, de l’huile et du miel. Et il s’arrêta et ne les tua pas avec leurs frères.
9 To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
Or la fosse dans laquelle Ismahel avait jeté tous les cadavres des hommes qu’il tua à cause de Godolias, est celle-là même qu’avait faite le roi Asa à cause de Baasa, roi d’Israël; Ismahel, fils de Nathanias, la remplit de morts.
10 Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
Et Ismahel fit prisonniers tous les restes du peuple qui étaient à Masphath, les filles du roi et tout le peuple qui était demeuré à Masphath, que Nabuzardan, prince de la milice, avait recommandés à Godolias, fils d’Ahicam. Et Ismahel, fils de Nathanias, les prit, et s’en alla afin de passer vers les enfants d’Ammon.
11 Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
Mais Johanan, fils de Carée, et tous les princes des hommes de guerre qui étaient avec lui, apprirent tout le mal qu’avait fait Ismahel, fils de Nathanias.
12 sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
Et ayant pris tous les hommes de guerre, ils partirent afin de combattre Ismahel, fils de Nathanias, et ils le trouvèrent près des grandes eaux qui sont à Gabaon.
13 Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
Et lorsque tout le peuple qui était avec Ismahel eut vu Johanan, fils de Carée, et tous les princes des hommes de guerre qui étaient avec lui, ils se réjouirent.
14 Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
Et tout le peuple qu’Ismahel avait pris à Masphath retourna; et, étant retourné, il vint vers Johanan, fils de Carée.
15 Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
Mais Ismahel, fils de Nathanias, s’enfuit avec huit hommes de devant la face de Johanan, et s’en alla vers les enfants d’Ammon.
16 Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
Johanan, fils de Carée, et tous les princes des hommes de guerre qui étaient avec lui, prirent donc tous les restes du peuple qu’il avait retirés des mains d’Ismahel, fils de Nathanias, et ramenés de Masphath, après qu’il eut tué Godolias, fils d’Ahicam; tous les hommes vaillants au combat et les femmes, les enfants et les eunuques qu’il avait ramenés de Gabaon.
17 Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
Et ils s’en allèrent, et ils s’arrêtèrent en passant à Chamaam, près de Bethléhem, afin de se rendre et d’entrer en Egypte,
18 don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.
À cause des Chaldéens; car ils les craignaient, parce qu’Ismahel, fils de Nathanias, avait tué Godolias, fils d’Ahicam, qu’avait préposé le roi de Babylone sur la terre de Juda.

< Irmiya 41 >