< Irmiya 41 >

1 A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
Or il arriva au septième mois qu'Ismaël fils de Néthania, fils d'Elisamah, de la race royale, et l'un des principaux de chez le Roi, et dix hommes avec lui, vinrent vers Guédalia fils d'Ahikam à Mitspa, et mangèrent là du pain ensemble à Mitspa.
2 sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
Mais Ismaël fils de Néthania se leva, et les dix hommes qui étaient avec lui, et ils frappèrent avec l'épée Guédalia fils d'Ahikam, fils de Saphan, et on le fit mourir, lui que le Roi de Babylone avait commis sur le pays.
3 Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
Ismaël frappa aussi tous les Juifs qui étaient avec lui, [c'est-à-dire], avec Guédalia à Mitspa, et les Caldéens, gens de guerre, qui furent trouvés là.
4 Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
Et il arriva que le jour après qu'on eut fait mourir Guédalia, avant que personne le sût,
5 sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
Quelques hommes de Sichem, de Silo, et de Samarie; en tout quatre-vingts hommes, ayant la barbe rasée, les vêtements déchirés, et s'étant fait des incisions, vinrent avec des dons et de l'encens dans leurs mains pour les apporter en la maison de l'Eternel.
6 Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
Alors Ismaël fils de Néthania sortit de Mitspa au devant d'eux, et il marchait en pleurant, et quand il les eut rencontrés, il leur dit: venez vers Guédalia fils d'Ahikam.
7 Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
Mais sitôt qu'ils furent venus au milieu de la ville, Ismaël fils de Néthania, accompagné des hommes qui étaient avec lui, les égorgea, [et les jeta] dans une fosse.
8 Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
Mais il se trouva dix hommes entre eux qui dirent à Ismaël: ne nous fais point mourir, car nous avons dans les champs des amas secrets de froment, d'orge, d'huile, et de miel; et il les laissa, et ne les fit point mourir avec leurs frères.
9 To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
Et la fosse dans laquelle Ismaël jeta les corps morts des hommes qu'il tua à l'occasion de Guédalia est celle que le Roi Asa avait fait faire lorsqu'il eut peur de Bahasa Roi d'Israël; et Ismaël fils de Néthania la remplit de gens tués.
10 Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
Et Ismaël emmena prisonniers tous ceux du peuple qui étaient demeurés de reste à Mitspa, [savoir] les filles du Roi, et tout le peuple qui était demeuré de reste à Mitspa, que Nébuzar-adan prévôt de l'hôtel avait commis à Guédalia fils d'Ahikam; Ismaël, dis-je, fils de Néthania, les emmenait prisonniers, et s'en allait pour passer vers les enfants de Hammon.
11 Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
Mais Johanan fils de Karéah, et tous les Capitaines des gens de guerre qui étaient avec lui, ayant entendu tout le mal qu'Ismaël fils de Néthania avait fait;
12 sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
Et ayant pris tous leurs gens ils s'en allèrent pour combattre contre Ismaël fils de Néthania, lequel ils rencontrèrent près des grosses eaux qui sont à Gabaon.
13 Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
Et il arriva qu'aussitôt que tout le peuple qui était avec Ismaël eut vu Johanan fils de Karéah, et tous les Capitaines des gens de guerre qui [étaient] avec lui, ils s'en réjouirent.
14 Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
Et tout le peuple qu'Ismaël emmenait prisonnier de Mitspa tourna visage, et se retournant ils s'en allèrent vers Johanan fils de Karéah.
15 Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
Mais Ismaël fils de Néthania échappa avec huit hommes de devant Johanan, et s'en alla vers les enfants de Hammon.
16 Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
Et Johanan fils de Karéah, et tous les Capitaines des gens de guerre qui étaient avec lui prirent tout le reste du peuple qu'ils avaient retiré des mains d'Ismaël fils de Néthania, [qu'il emmenait prisonnier] de Mitspa, après qu'il eut frappé Guédalia fils d'Ahikam, [savoir] les vaillants hommes de guerre, et les femmes, et les enfants, et les Eunuques; et les ramenèrent de Gabaon.
17 Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
Et ils s'en allèrent et demeurèrent à Guéruth-kimham, auprès de Bethléhem, pour s'en aller et se retirer en Egypte,
18 don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.
A cause des Caldéens; car ils avaient peur d'eux, parce qu'Ismaël fils de Néthania avait tué Guédalia fils d'Ahikam, qui avait été commis sur le pays par le Roi de Babylone.

< Irmiya 41 >