< Irmiya 41 >

1 A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
And it came to pass in the seventh month, that Ismahel the son of Nathanias, the son of Elisama of the royal blood, and the nobles of the king, and ten men with him, came to Godolias the son of Ahicam into Masphath: and they ate bread there together in Masphath.
2 sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
And Ismahel the son of Nathanias arose, and the ten men that were with him, and they struck Godolias the son of Ahicam, the son of Saphan with the sword, and slew him whom the king of Babylon had made governor over the land.
3 Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
Ismahel slew also all the Jews that were with Godolias in Masphath, and the Chaldeans that were found there, and the soldiers.
4 Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
And on the second day after he had killed Godolias, no man yet knowing it,
5 sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
There came some from Sichem, and from Silo, and from Samaria, fourscore men, with their beards shaven, and their clothes rent, and mourning: and they had offerings and incense in their hand, to offer in the house of the Lord.
6 Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
And Ismahel the son of Nathanias went forth from Masphath to meet them, weeping all along as he went: and when he had met them, he said to them: Come to Godolias, the son of Ahicam.
7 Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
And when they were come to the midst of the city, Ismahel the son of Nathanias, slew them, and cast them into the midst of the pit, he and the men that were with him.
8 Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
But ten men were found among them, that said to Ismahel: Kill us not: for we have stores in the field, of wheat, and barley, and oil, and honey. And he forbore, and slew them not with their brethren.
9 To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
And the pit into which Ismahel cast all the dead bodies of the men whom he slew because of Godolias, is the same that king Asa made, for fear of Baasa the king of Israel: the same did Ismahel the son of Nathanias fill with them that were slain.
10 Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
Then Ismahel carried away captive all the remnant of the people that were in Masphath: the king’s daughters, and all the people that remained in Masphath: whom Nabuzardan the general of the army had committed to Godolias the son of Ahicam. And Ismahel the son of Nathanias took them, and he departed, to go over to the children of Ammon.
11 Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
But Johanan the son of Caree, and all the captains of the fighting men that were with him, heard of the evil that Ismahel the son of Nathanias had done.
12 sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
And taking all the men, they went out to fight against Ismahel the son of Nathanias, and they found him by the great waters that are in Gabaon.
13 Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
And when all the people that were with Ismahel, had seen Johanan the son of Caree, and all the captains of the fighting men that were with him, they rejoiced.
14 Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
And all the people whom Ismahel had taken, went back to Masphath: and they returned and went to Johanan the son of Caree.
15 Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
But Ismahel the son of Nathanias fled with eight men, from the face of Johanan, and went to the children of Ammon.
16 Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
Then Johanan the son of Caree, and all the captains of the soldiers that were with him, took all the remnant of the people whom they had recovered from Ismahel the son of Nathanias, from Masphath, after that he had slain Godolias the son of Ahicam: valiant men for war, and the women, and the children, and the eunuchs, whom he had brought back from Gabaon:
17 Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
And they departed, and sat as sojourners in Chamaam, which is near Bethlehem: in order to go forward, and enter into Egypt,
18 don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.
From the face of the Chaldeans: for they were afraid of them, because Ismahel the son of Nathanias had slain Godolias the son of Ahicam, whom the king of Babylon had made governor in the land of Juda.

< Irmiya 41 >