< Irmiya 40 >

1 Sai magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya sake shi a Rama. Ya sami Irmiya a daure da sarƙoƙi a cikin sauran kamammu daga Urushalima da kuma Yahuda waɗanda ake kaiwa zaman bauta a Babilon.
A palavra que veio de Javé a Jeremias, depois que Nebuzaradan o capitão da guarda o havia libertado de Ramá, quando o havia levado acorrentado entre todos os cativos de Jerusalém e Judá que foram levados em cativeiro para a Babilônia.
2 Sa’ad da shugaban matsaran ya sami Irmiya sai ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ya sa wannan masifa saboda wannan wuri.
O capitão da guarda levou Jeremias e lhe disse: “Yahweh seu Deus pronunciou este mal neste lugar;
3 Yanzu kuma Ubangiji ya cika shi; ya yi kamar yadda ya faɗa. Dukan wannan ya faru domin kun yi zunubi ga Ubangiji ba ku kuwa yi masa biyayya ba.
e Yahweh o trouxe, e fez de acordo com o que ele falou. Porque você pecou contra Javé, e não obedeceu a sua voz, portanto, esta coisa veio sobre você”.
4 Amma yau ina’yantar da kai daga sarƙoƙin da suke a hannuwanka. Zo mu tafi Babilon, in kana so, zan kuwa lura da kai; amma in ba ka so, kada ka zo. Ga shi, dukan ƙasar tana a gabanka; ka tafi duk inda ka so.”
Agora, eis que hoje eu o liberto das correntes que estão em sua mão. Se lhe parece bom vir comigo à Babilônia, venha, e eu cuidarei de você; mas se lhe parece mau vir comigo à Babilônia, não o faça. Eis que toda a terra está diante de você. Onde lhe parece bom e correto ir, vá para lá”.
5 Amma, kafin Irmiya yă juya yă tafi, Nebuzaradan ya ƙara da cewa, “Ka koma wurin Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, wanda sarkin Babilon ya naɗa a kan garuruwan Yahuda, ka zauna da shi a cikin mutane, ko kuwa ka tafi duk inda ka ga dama.” Sa’an nan shugaban ya ba shi abinci da kuma kyauta sai ya bar shi ya tafi.
Agora, enquanto ele ainda não tinha voltado, “Volte então”, disse ele, “para Gedaliah, o filho de Ahikam, o filho de Shaphan, a quem o rei da Babilônia nomeou governador das cidades de Judá, e habitar com ele entre o povo; ou vá para onde lhe pareça certo ir”. Então o capitão da guarda lhe deu comida e um presente, e o deixou ir.
6 Saboda haka Irmiya ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa ya zauna tare da shi a cikin mutanen da aka bari a ƙasar.
Então Jeremias foi para Gedaliah, filho de Ahikam, para Mizpah, e viveu com ele entre as pessoas que ficaram na terra.
7 Sa’ad da dukan shugabannin hafsoshin tare da mutanen da suke a karkara suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya ɗan Ahikam gwamna a kan ƙasar ya kuma sa shi ya lura da maza, mata da’ya’yan da suke mafi talauci a ƙasar da waɗanda ba a kwashe zuwa zaman bauta a Babilon ba,
Agora, quando todos os capitães das forças que estavam nos campos, mesmo eles e seus homens, ouviram que o rei da Babilônia havia feito de Gedalias o filho do governador de Ahikam na terra, e se comprometeram com ele homens, mulheres, crianças, e dos mais pobres da terra, daqueles que não foram levados cativos para Babilônia,
8 sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan da Yonatan’ya’yan Kareya, da Serahiya ɗan Tanhumet maza,’ya’yan Efai maza, mutumin Netofa, da Yezaniya ɗan mutumin Ma’aka da mutanensu.
então Ismael, filho de Netanias, e Johananan e Jonathan, filhos de Kareah, e Seraías, filho de Tanhumeth, e os filhos de Ephai, o netofatita, e Jezanias, filho do maacatita, eles e seus homens vieram para Gedaliah, para Mizpah.
9 Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, ya yi rantsuwa don yă tabbatar musu da mutanensu. Ya ce, “Kada ku ji tsoron bauta wa Babiloniyawa. Ku zauna a ƙasar ku bauta wa sarkin Babilon, zai kuma yi muku amfani.
Gedaliah o filho de Ahikam o filho de Shaphan jurou a eles e aos seus homens, dizendo: “Não tenham medo de servir aos caldeus. Habite na terra, e sirva o rei da Babilônia, e estará bem com você.
10 Ni kaina zan zauna a Mizfa in zama wakilinku a gaban Babiloniyawa waɗanda za su zo wurinmu, amma ku girbe ruwan inabi,’ya’yan itatuwa na kaka, da mai, ku zuba su a tulunan ajiyarku, ku kuma zauna a garuruwan da kuka ci.”
Quanto a mim, eis que habitarei em Mizpah, para estar diante dos caldeus que virão até nós; mas vós, colhei vinho e frutas de verão e azeite, e colocai-os em vossas embarcações, e habitai em vossas cidades que tomastes”.
11 Sa’ad da dukan Yahudawan da suke a Mowab, Ammon, Edom da sauran ƙasashe suka ji cewa sarkin Babilon ya bar raguwa a Yahuda ya kuma naɗa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan gwamna a kansu,
Da mesma forma, quando todos os judeus que estavam em Moab, e entre as crianças de Amon, e em Edom, e que estavam em todos os países, ouviram que o rei da Babilônia havia deixado um remanescente de Judá, e que ele havia colocado sobre eles Gedalias, filho de Ahikam, filho de Shaphan,
12 sai suka dawo ƙasar Yahuda, wurin Gedaliya a Mizfa, daga dukan ƙasashen da suke a warwatse. Suka girbe ruwan inabi a yalwace da’ya’yan itatuwan kaka.
então todos os judeus voltaram de todos os lugares onde foram expulsos, e vieram para a terra de Judá, para Gedalias, para Mizpah, e colheram muito vinho e frutas de verão.
13 Yohanan ɗan Kareya da dukan manyan sojoji da suke a karkara suka zo wurin Gedaliya a Mizfa
Moreover Johanan o filho de Kareah, e todos os capitães das forças que estavam nos campos, vieram a Gedaliah para Mizpah,
14 suka ce masa, “Ba ka san cewa Ba’alis sarkin Ammonawa ya aiki Ishmayel ɗan Netaniya ya ɗauke ranka ba?” Amma Gedaliya ɗan Ahikam bai gaskata su ba.
e lhe disseram: “Você sabe que Baalis, o rei dos filhos de Amon, enviou Ismael, o filho de Nethaniah, para tirar sua vida”? Mas Gedaliah, o filho de Ahikam, não acreditava neles.
15 Sai Yohanan ɗan Kareya ya yi wa Gedaliya a Mizfa magana a asirce ya ce, “Bari in tafi in kashe Ishmayel ɗan Netaniya, ba kuwa wanda zai sani. Me zai sa ya ɗauke ranka ya watsar da dukan Yahudawan da suka taru kewaye da kai har waɗanda suka ragu na Yahuda su hallaka?”
Então Johanan, o filho de Kareah, falou em segredo com Gedaliah em Mizpah, dizendo: “Por favor, deixe-me ir, e eu matarei Ismael, o filho de Nethaniah, e nenhum homem saberá disso”. Por que ele deveria tirar sua vida, para que todos os judeus que estão reunidos a você sejam dispersos, e o remanescente de Judá pereça”?
16 Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohanan ɗan Kareya, “Kada ka yi irin wannan abu! Abin da kake faɗa game da Ishmayel ba gaskiya ba ne.”
Mas Gedaliah, filho de Ahikam, disse a Johanan o filho de Kareah: “Você não fará isso, pois fala falsamente de Ismael”.

< Irmiya 40 >