< Irmiya 40 >

1 Sai magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya sake shi a Rama. Ya sami Irmiya a daure da sarƙoƙi a cikin sauran kamammu daga Urushalima da kuma Yahuda waɗanda ake kaiwa zaman bauta a Babilon.
La parole qui vint à Jérémie de par l’Éternel, après que Nebuzaradan, chef des gardes, l’eut renvoyé de Rama, quand il l’eut pris, et qu’il était lié de chaînes au milieu de tous les captifs de Jérusalem et de Juda qu’on transportait à Babylone.
2 Sa’ad da shugaban matsaran ya sami Irmiya sai ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ya sa wannan masifa saboda wannan wuri.
Et le chef des gardes prit Jérémie, et lui dit: L’Éternel, ton Dieu, avait prononcé ce mal sur ce lieu-ci.
3 Yanzu kuma Ubangiji ya cika shi; ya yi kamar yadda ya faɗa. Dukan wannan ya faru domin kun yi zunubi ga Ubangiji ba ku kuwa yi masa biyayya ba.
Et l’Éternel l’a fait venir, et a fait comme il avait dit, car vous avez péché contre l’Éternel, et vous n’avez pas écouté sa voix; et cette chose vous est arrivée.
4 Amma yau ina’yantar da kai daga sarƙoƙin da suke a hannuwanka. Zo mu tafi Babilon, in kana so, zan kuwa lura da kai; amma in ba ka so, kada ka zo. Ga shi, dukan ƙasar tana a gabanka; ka tafi duk inda ka so.”
Et maintenant, voici, aujourd’hui je te délivre des chaînes qui sont à tes mains. S’il est bon à tes yeux de venir avec moi à Babylone, viens, et j’aurai les yeux sur toi; mais, s’il est mauvais à tes yeux de venir avec moi à Babylone, ne viens pas. Regarde, toute la terre est devant toi: va où il est bon et droit à tes yeux d’aller.
5 Amma, kafin Irmiya yă juya yă tafi, Nebuzaradan ya ƙara da cewa, “Ka koma wurin Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, wanda sarkin Babilon ya naɗa a kan garuruwan Yahuda, ka zauna da shi a cikin mutane, ko kuwa ka tafi duk inda ka ga dama.” Sa’an nan shugaban ya ba shi abinci da kuma kyauta sai ya bar shi ya tafi.
Et comme encore il ne répondait pas, [Nebuzaradan lui dit]: Retourne-t’en vers Guedalia, fils d’Akhikam, fils de Shaphan, que le roi de Babylone a établi sur les villes de Juda, et demeure avec lui au milieu du peuple, ou va partout où il sera bon à tes yeux d’aller. Et le chef des gardes lui donna des provisions et un présent, et le renvoya.
6 Saboda haka Irmiya ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa ya zauna tare da shi a cikin mutanen da aka bari a ƙasar.
Et Jérémie vint vers Guedalia, fils d’Akhikam, à Mitspa, et habita avec lui parmi le peuple qui était de reste dans le pays.
7 Sa’ad da dukan shugabannin hafsoshin tare da mutanen da suke a karkara suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya ɗan Ahikam gwamna a kan ƙasar ya kuma sa shi ya lura da maza, mata da’ya’yan da suke mafi talauci a ƙasar da waɗanda ba a kwashe zuwa zaman bauta a Babilon ba,
Et tous les chefs des forces qui étaient dans la campagne, eux et leurs hommes, apprirent que le roi de Babylone avait établi Guedalia, fils d’Akhikam, sur le pays, et qu’il lui avait confié les hommes, et les femmes, et les enfants, et des pauvres du pays d’entre ceux qui n’avaient pas été transportés à Babylone;
8 sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan da Yonatan’ya’yan Kareya, da Serahiya ɗan Tanhumet maza,’ya’yan Efai maza, mutumin Netofa, da Yezaniya ɗan mutumin Ma’aka da mutanensu.
et ils vinrent vers Guedalia à Mitspa, savoir Ismaël, fils de Nethania, et Jokhanan et Jonathan, les fils de Karéakh, et Seraïa, fils de Thanhumeth, et les fils d’Éphaï, le Netophathite, et Jezania, fils d’un Maacathien, eux et leurs hommes.
9 Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, ya yi rantsuwa don yă tabbatar musu da mutanensu. Ya ce, “Kada ku ji tsoron bauta wa Babiloniyawa. Ku zauna a ƙasar ku bauta wa sarkin Babilon, zai kuma yi muku amfani.
Et Guedalia, fils d’Akhikam, fils de Shaphan, leur jura, à eux et à leurs hommes, disant: Ne craignez pas de servir les Chaldéens; habitez dans le pays et servez le roi de Babylone, et vous vous en trouverez bien.
10 Ni kaina zan zauna a Mizfa in zama wakilinku a gaban Babiloniyawa waɗanda za su zo wurinmu, amma ku girbe ruwan inabi,’ya’yan itatuwa na kaka, da mai, ku zuba su a tulunan ajiyarku, ku kuma zauna a garuruwan da kuka ci.”
Et pour moi, voici, j’habite à Mitspa, pour me tenir là devant les Chaldéens qui viendront vers nous; et vous, récoltez du vin, et des fruits d’été, et de l’huile, et mettez-les dans vos vases, et habitez dans vos villes dont vous avez pris possession.
11 Sa’ad da dukan Yahudawan da suke a Mowab, Ammon, Edom da sauran ƙasashe suka ji cewa sarkin Babilon ya bar raguwa a Yahuda ya kuma naɗa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan gwamna a kansu,
Et aussi tous les Juifs qui étaient en Moab, et parmi les fils d’Ammon, et en Édom, ou qui étaient dans tous les pays, entendirent que le roi de Babylone avait accordé un reste à Juda, et qu’il avait établi sur eux Guedalia, fils d’Akhikam, fils de Shaphan;
12 sai suka dawo ƙasar Yahuda, wurin Gedaliya a Mizfa, daga dukan ƙasashen da suke a warwatse. Suka girbe ruwan inabi a yalwace da’ya’yan itatuwan kaka.
alors tous les Juifs retournèrent de tous les lieux où ils avaient été chassés, et vinrent dans le pays de Juda, vers Guedalia, à Mitspa, et récoltèrent du vin et des fruits d’été en grande abondance.
13 Yohanan ɗan Kareya da dukan manyan sojoji da suke a karkara suka zo wurin Gedaliya a Mizfa
Mais Jokhanan, fils de Karéakh, et tous les chefs des forces qui étaient dans la campagne, vinrent vers Guedalia, à Mitspa,
14 suka ce masa, “Ba ka san cewa Ba’alis sarkin Ammonawa ya aiki Ishmayel ɗan Netaniya ya ɗauke ranka ba?” Amma Gedaliya ɗan Ahikam bai gaskata su ba.
et lui dirent: Sais-tu bien que Baalis, roi des fils d’Ammon, a envoyé Ismaël, fils de Nethania, pour te frapper à mort? Mais Guedalia, fils d’Akhikam, ne les crut point.
15 Sai Yohanan ɗan Kareya ya yi wa Gedaliya a Mizfa magana a asirce ya ce, “Bari in tafi in kashe Ishmayel ɗan Netaniya, ba kuwa wanda zai sani. Me zai sa ya ɗauke ranka ya watsar da dukan Yahudawan da suka taru kewaye da kai har waɗanda suka ragu na Yahuda su hallaka?”
Et Jokhanan, fils de Karéakh, parla en secret à Guedalia, à Mitspa, disant: Que j’aille, je te prie, et je frapperai Ismaël, fils de Nethania, et personne ne le saura; pourquoi te frapperait-il à mort, et tous ceux de Juda qui se sont rassemblés vers toi seraient-ils dispersés, et le reste de Juda périrait-il?
16 Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohanan ɗan Kareya, “Kada ka yi irin wannan abu! Abin da kake faɗa game da Ishmayel ba gaskiya ba ne.”
Et Guedalia, fils d’Akhikam, dit à Jokhanan, fils de Karéakh: Ne fais pas cette chose-là, car c’est un mensonge que tu dis à l’égard d’Ismaël.

< Irmiya 40 >