< Irmiya 4 >

1 “In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
Si tu reviens, ô Israël, dit l’Éternel, reviens à moi; et si tu ôtes tes abominations de devant moi, tu ne seras plus errant,
2 kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
et tu jureras en vérité, en jugement et en justice: L’Éternel est vivant! Et les nations se béniront en lui, et en lui elles se glorifieront.
3 Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
Car ainsi dit l’Éternel aux hommes de Juda et à Jérusalem: Défrichez pour vous un terrain neuf, et ne semez pas au milieu des épines.
4 Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
Circoncisez-vous pour l’Éternel, et ôtez le prépuce de vos cœurs, hommes de Juda et habitants de Jérusalem, de peur que ma fureur ne sorte comme un feu et ne brûle, sans qu’il y ait personne pour l’éteindre, à cause de l’iniquité de vos actions.
5 “Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
Annoncez en Juda, et faites entendre dans Jérusalem, et dites, … et sonnez de la trompette dans le pays; criez à plein gosier et dites: Assemblez-vous, et entrons dans les villes fortes.
6 Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
Élevez l’étendard vers Sion, fuyez, et ne vous arrêtez pas; car je fais venir du nord le mal et une grande ruine.
7 Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
Le lion est monté de son fourré, et le destructeur des nations s’est mis en chemin; il est sorti de son lieu pour mettre ton pays en désolation: tes villes seront dévastées, de sorte qu’il n’y aura pas d’habitant.
8 Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
C’est pourquoi ceignez-vous de sacs, lamentez-vous, et hurlez; car l’ardeur de la colère de l’Éternel ne s’est point détournée de nous.
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
Et il arrivera en ce jour-là, dit l’Éternel, que le cœur du roi défaillira et le cœur des princes, et que les sacrificateurs seront étonnés, et les prophètes stupéfaits.
10 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
Et je dis: Ah, Seigneur Éternel! certainement tu as bien trompé ce peuple et Jérusalem, en disant: Vous aurez la paix!… et l’épée est venue jusqu’à l’âme.
11 A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
En ce temps-là, il sera dit à ce peuple et à Jérusalem: Un vent sec [vient] des hauteurs du désert, dans le chemin de la fille de mon peuple, non pour vanner, ni pour purifier.
12 iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
Un vent plus véhément que celui-là viendra de par moi; maintenant, moi aussi je prononcerai [mes] jugements sur eux.
13 Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
Voici, il monte comme des nuées, et ses chars sont comme un tourbillon; ses chevaux, plus rapides que les aigles. Malheur à nous! car nous sommes détruits.
14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
Lave ton cœur de l’iniquité, Jérusalem, afin que tu sois sauvée! Jusques à quand tes vaines pensées demeureront-elles au-dedans de toi?
15 Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
Car une voix annonce de Dan, et, de la montagne d’Éphraïm, publie l’affliction.
16 “A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
Faites savoir aux nations; voici, faites entendre à Jérusalem: Des assiégeants viennent d’un pays lointain et font retentir leur voix contre les villes de Juda.
17 Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
Ils sont tout autour d’elle comme ceux qui gardent un champ; car elle s’est rebellée contre moi, dit l’Éternel.
18 “Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
Ta voie et tes actions ont amené sur toi ces choses, c’est là ton iniquité; oui, c’est [une chose] amère; oui, elle pénètre jusqu’à ton cœur.
19 Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
Mes entrailles! mes entrailles! je suis dans la douleur! Les parois de mon cœur! Mon cœur bruit au-dedans de moi, je ne puis me taire; car, mon âme, tu entends le son de la trompette, la clameur de la guerre!
20 Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
Ruine sur ruine se fait entendre, car tout le pays est dévasté: soudain mes tentes sont dévastées, en un moment, mes courtines.
21 Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
Jusques à quand verrai-je l’étendard, entendrai-je la voix de la trompette?
22 “Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
Car mon peuple est fou, ils ne m’ont pas connu; ce sont des fils insensés, ils n’ont pas d’intelligence; ils sont sages pour faire le mal, mais ils ne savent pas faire le bien.
23 Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
J’ai regardé la terre, et voici, elle était désolation et vide, et vers les cieux, et leur lumière n’était pas.
24 Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
J’ai regardé les montagnes, et voici, elles se remuaient, et toutes les collines branlaient.
25 Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
J’ai regardé, et voici, il n’y avait pas d’homme, et tous les oiseaux des cieux avaient fui.
26 Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
J’ai regardé, et voici, le Carmel était un désert, et toutes ses villes étaient renversées devant l’Éternel, devant l’ardeur de sa colère.
27 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
Car ainsi dit l’Éternel: Tout le pays sera une désolation, mais je ne le détruirai pas entièrement.
28 Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
À cause de cela, la terre mènera deuil, et, au-dessus, les cieux seront noirs, parce que je l’ai dit, je l’ai pensé, et je ne m’en repentirai point et je n’en reviendrai point.
29 Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
Devant le bruit des cavaliers et des tireurs d’arc toute ville fuit: ils entrent dans les fourrés et montent sur les rochers; toute ville est abandonnée, et aucun homme n’y habite.
30 Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
Et toi, dévastée, que feras-tu? Tu as beau te revêtir d’écarlate, te parer d’ornements d’or, te déchirer les yeux avec du fard, tu te fais belle en vain: les amants te méprisent, ils cherchent ta vie.
31 Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”
Car j’ai entendu une voix comme celle d’une femme en travail, une angoisse comme d’une femme enfantant son premier-né, la voix de la fille de Sion; elle soupire, elle étend ses mains: Malheur à moi! car mon âme a défailli à cause des meurtriers!

< Irmiya 4 >