< Irmiya 4 >

1 “In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
Israel, if thou turnest ayen, seith the Lord, turne thou to me; if thou takist awei thin offendyngis fro my face, thou schalt not be mouyd.
2 kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
And thou schalt swere, The Lord lyueth, in treuthe and in doom and in riytfulnesse; and alle folkis schulen blesse hym, and schulen preise hym.
3 Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
For the Lord God seith these thingis to a man of Juda and to a dwellere of Jerusalem, Make ye newe to you a lond tilid of the newe, and nyle ye sowe on thornes.
4 Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
Men of Juda, and dwelleris of Jerusalem, be ye circumcidid to the Lord, and do ye awey the filthis of youre hertis; lest perauenture myn indignacioun go out as fier, and be kyndlid, and noon be that quenche, for the malice of youre thouytis.
5 “Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
Telle ye in Juda, and make ye herd in Jerusalem; speke ye, and synge ye with a trumpe in the lond; crye ye strongli, and seie ye, Be ye gaderid togidere, and entre we in to stronge citees.
6 Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
Reise ye a signe in Sion, coumforte ye, and nyle ye stonde; for Y bringe yuel fro the north, and a greet sorewe.
7 Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
A lioun schal `rise vp fro his denne, and the robbere of folkis schal reise hym silf. He is goon out of his place, to sette thi lond in to wildirnesse; thi citees schulen be distried, abidynge stille with out dwellere.
8 Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
On this thing girde you with heiris; weile ye, and yelle, for the wraththe of the strong veniaunce of the Lord is not turned awei fro you.
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
And it schal be, in that dai, seith the Lord, the herte of the king schal perische, and the herte of princis; and the prestis schulen wondre, and the prophetis schulen be astonyed.
10 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
And Y seide, Alas! alas! alas! Lord God; therfor whether thou hast disseyued this puple and Jerusalem, seiynge, Pees schal be to you, and lo! a swerd is comun `til to the soule?
11 A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
In that tyme it schal be seide to this puple and to Jerusalem, A brennynge wynd in the weies that ben in desert, ben the weies of the douytir of my puple, not to wyndewe, and not to purge.
12 iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
A spirit ful of hem schal come to me; and now Y, but Y schal speke my domes with hem.
13 Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
Lo! he schal stie as a cloude, and hise charis as a tempest; hise horsis ben swifter than eglis; wo to vs, for we ben distried.
14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
Thou Jerusalem, waische thin herte fro malice, that thou be maad saaf. Hou long schulen noiful thouytis dwelle in thee?
15 Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
For whi the vois of a tellere fro Dan, and makynge knowun an idol fro the hil of Effraym.
16 “A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
Reise, ye folkis; lo! it is herd in Jerusalem that keperis ben comun fro a fer lond, and yyuen her vois on the citees of Juda.
17 Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
As the keperis of feeldis thei ben maad on it in cumpas; for it stiride me to wrathfulnesse, seith the Lord.
18 “Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
Thi weyes and thi thouytis han maad this to thee; this malice of thee, for it is bittir, for it touchide thin herte.
19 Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
Mi wombe akith, my wombe akith; the wittis of myn herte ben disturblid in me. Y schal not be stille, for my soule herde the vois of a trumpe, the cry of batel.
20 Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
Sorewe is clepid on sorewe, and al the lond is distried; my tabernaclis ben wastid sudeynli, my skynnes ben wastid sudeynli.
21 Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
Hou longe schal Y se hem that fleen, schal Y here the vois of a clarioun?
22 “Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
For my fonned puple knew not me; thei ben vnwise sones, and cowardis; thei ben wise to do yuels, but thei kouden not do wel.
23 Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
Y bihelde the lond, and lo! it was void, and nouyt; and Y bihelde heuenes, and no liyt was in tho.
24 Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
Y siy munteyns, and lo! tho weren mouyd, and all litle hillis weren disturblid.
25 Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
Y lokide, and no man was, and ech brid of heuene was gon a wey.
26 Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
Y bihelde, and lo! Carmele is forsakun, and alle citees therof ben distried fro the face of the Lord, and fro the face of the ire of his strong veniaunce.
27 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
For the Lord seith these thingis, Al the lond schal be forsakun, but netheles Y schal not make an endyng.
28 Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
The erthe schal mourne, and heuenys aboue schulen make sorewe, for that Y spak; Y thouyte, and it repentide not me, nether Y am turned awei fro it.
29 Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
Ech citee fledde fro the vois of a knyyt, and of a man schetynge an arowe; thei entriden in to hard places, and stieden in to roochis of stoon; alle citees ben forsakun, and no man dwellith in tho.
30 Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
But what schalt thou `destried do? Whanne thou schalt clothe thee with reed scarlet, whanne thou schalt be ourned with a goldun broche, and schalt anoynte thin iyen with wommans oynement, thou schalt be araied in veyn; thi louyeris han dispisid thee, thei schulen seke thi soule.
31 Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”
For Y herd a vois as of a womman trauelynge of child, the angwischis as of a womman childynge; the vois of the douyter of Sion among hem that dien, and spreden abrood her hondis; Wo to me, for my soule failide for hem that ben slayn.

< Irmiya 4 >