< Irmiya 4 >
1 “In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
“If you return, Israel—this is Yahweh's declaration—then it should be to me that you return. If you remove your detestable things from before me and do not wander from me again,
2 kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
You must be truthful, just, and righteous when you swear, 'As Yahweh lives.' Then the nations will bless themselves in him, and in him they will glory.”
3 Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
For Yahweh says this to each person in Judah and Jerusalem: 'Plow your own ground, and do not sow among thorns.
4 Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
Circumcise yourselves to Yahweh, and remove the foreskins of your heart, men of Judah and inhabitants of Jerusalem, or else my fury will break out like fire, and burn with no one to quench it, because of the wickedness of your deeds.
5 “Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
Report in Judah and let it be heard in Jerusalem. Say, “Blow the trumpet in the land.” Proclaim, “Gather together. Let us go to the fortified cities.”
6 Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
Lift up the signal flag and point it toward Zion, and run for safety! Do not stay, for I am bringing disaster from the north and a great collapse.
7 Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
A lion is coming out from his thicket and someone who will destroy nations is setting out. He is leaving his place to bring horror to your land, to turn your cities into ruins, where no one will live.
8 Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
Because of this, wrap yourself in sackcloth, lament and wail. For the force of Yahweh's anger has not turned away from us.
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
Then it will happen in that day—this is Yahweh's declaration—that the hearts of the king and his officials will die. The priests will be appalled, and the prophets will be horrified.'”
10 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
So I said, “Ah! Lord Yahweh. Surely you have completely deceived this people and Jerusalem by saying, 'There will be peace for you.' Yet the sword is striking against their life.”
11 A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
In that time it will be said of this people and Jerusalem, “A burning wind from the plains of the desert will make its way to the daughter of my people. It will not winnow or cleanse them.
12 iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
A wind far stronger than that will come at my command, and I will now pass sentence against them.
13 Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
See, he is attacking like clouds, and his chariots are like a storm. His horses are faster than eagles. Woe to us, for we will be devastated!
14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
Cleanse your heart from wickedness, Jerusalem, so that you might be saved. How long will your deepest thoughts be about how to sin?
15 Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
For a voice is bringing news from Dan, and the coming disaster is heard from the mountains of Ephraim.
16 “A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
Make the nations think about this: See, announce to Jerusalem that besiegers are coming from a distant land to shout in battle against the cities of Judah.
17 Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
They will be like the watchmen of a cultivated field against her all around, since she has been rebellious against me—this is Yahweh's declaration—
18 “Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
and your conduct and your deeds have done these things to you. This will be your punishment. How terrible it will be! It will strike your very heart.
19 Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
My heart! My heart! I am in anguish in my heart. My heart is turbulent within me. I cannot keep quiet for I hear the sound of the horn, an alarm for battle.
20 Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
Disaster follows after disaster; for all the land lies in ruins. Suddenly my tents are destroyed, my curtains in a moment.
21 Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
How long will I see the standard? Will I hear the sound of the horn?
22 “Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
For the foolishness of my people—they do not know me. They are idiotic people and they have no understanding. They have skill at evil, but do not know to do good.
23 Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
I saw the land. Behold! It was formless and empty. For there was no light for the heavens.
24 Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
I looked at the mountains. Behold, they were trembling, and all the hills were shaking about.
25 Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
I looked. Behold, there was no one, and all the birds of the heavens had fled.
26 Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
I looked. Behold, the orchards were a wilderness and all the cities had been pulled down before Yahweh, before the fury of his wrath.”
27 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
This is what Yahweh says, “All the land will become a devastation, but I will not completely destroy it.
28 Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
For this reason, the land will mourn, and the heavens above will darken. For I have declared my intentions; I will not hold back; I will not turn from carrying them out.
29 Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
Every city will flee from the noise of the cavalry and the archers with a bow; they will run into the forests. Every city will climb up into the rocky places. The cities will be abandoned, for there will be no one to inhabit them.
30 Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
Now that you have been devastated, what will you do? For though you dress in scarlet, adorn yourself with gold jewelry, and make your eyes look bigger with paint, the men who lusted for you now reject you. Instead, they are trying to take away your life.
31 Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”
So I hear the sound of anguish, distress as in the birth of a firstborn child, the sound of the daughter of Zion. She is gasping for breath. She spreads out her hands, 'Woe to me! I am fainting because of these murderers.'”