< Irmiya 4 >
1 “In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
“If you return, O Israel,” A declaration of YHWH, “Return to Me, And if you turn aside Your abominations from My face, Then you do not bemoan.
2 kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
And you have sworn—YHWH lives, In truth, in judgment, and in righteousness, And nations have blessed themselves in Him, And they boast themselves in Him.”
3 Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
For thus said YHWH, To the man of Judah, and to Jerusalem: “Till for yourselves tillage, And do not sow to the thorns.
4 Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
Be circumcised to YHWH, And turn aside the foreskins of your heart, O man of Judah, and you inhabitants of Jerusalem, Lest My fury goes out as fire, and has burned, And there is none quenching, Because of the evil of your doings.”
5 “Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
Declare in Judah, and sound in Jerusalem, and say: “Blow a horn in the land, Call, Fill up together, And say, Assemble yourselves and let us go into the fortified cities.
6 Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
Lift up an ensign toward Zion, Strengthen yourselves, do not stand still, For I am bringing evil in from the north, And a great destruction.”
7 Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
A lion has gone up from his thicket, And a destroyer of nations has journeyed, He has come forth from his place To make your land become a desolation, Your cities are laid waste, without inhabitant.
8 Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
For this, gird on sackcloth, lament and howl, For the fierce anger of YHWH has not turned back from us.
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
“And it has come to pass in that day,” A declaration of YHWH, “The heart of the king perishes, And the heart of the princes, And the priests have been astonished, And the prophets wonder.”
10 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
And I say, “Aah! Lord YHWH, Surely you have entirely forgotten this people and Jerusalem, Saying, Peace is for you, And a sword has struck to the soul!”
11 A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
At that time it is said of this people, And of Jerusalem: “A dry wind of high places in the wilderness, The way of the daughter of My people (Not for winnowing, nor for cleansing),
12 iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
A full wind from these comes for Me, Now also, I speak judgments with them.”
13 Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
“Behold, he comes up as clouds, And his chariots as a windstorm, His horses have been lighter than eagles, Woe to us, for we have been spoiled.”
14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
Wash evil from your heart, O Jerusalem, That you may be saved, Until when do you lodge in your heart Thoughts of your strength?
15 Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
For a voice is declaring from Dan, And sounding sorrow from Mount Ephraim:
16 “A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
“Make mention to the nations, Behold, sound to Jerusalem, Besiegers are coming from the far-off land, And they give forth their voice against cities of Judah.
17 Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
As the keepers of a field They have been against her all around, For she has been rebellious with Me,” A declaration of YHWH.
18 “Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
“Your way and your doings have done these to you, This [is] your distress, for [it is] bitter, For it has struck to your heart.”
19 Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
My bowels, my bowels! I am pained [in] the walls of my heart, My heart makes a noise for me, I am not silent, For I have heard the voice of a horn, O my soul—a shout of battle!
20 Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
Destruction on destruction is proclaimed, For all the land has been spoiled, My tents have suddenly been spoiled, In a moment—my curtains.
21 Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
Until when do I see an ensign? Do I hear the voice of a horn?
22 “Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
“For My people [are] foolish, They have not known Me, They [are] foolish sons, Indeed, they [are] not intelligent, They [are] wise to do evil, And they have not known to do good.”
23 Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
I looked [to] the earth, and behold—formless and void, And to the heavens, and they [had] no light.
24 Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
I have looked [to] the mountains, And behold, they are trembling. And all the hills moved themselves lightly.
25 Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
I have looked, and behold, man is not, And all birds of the heavens have fled.
26 Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
I have looked, and behold, The fruitful place [is] a wilderness, And all its cities have been broken down, Because of YHWH, Because of the fierceness of His anger.
27 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
For thus said YHWH: “All the land is a desolation, but I do not make a completion.
28 Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
For this the earth mourns, And the heavens above have been black, Because I have spoken—I have purposed, And I have not relented, Nor do I turn back from it.
29 Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
From the voice of the horseman, And of him shooting with the bow, All the city is fleeing, They have come into thickets, And they have gone up on cliffs, All the city is forsaken, And there is no one dwelling in them.
30 Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
And you, O spoiled one, what do you do? For you put on scarlet, For you adorn yourself [with] ornaments of gold. For you tear your eyes with pain, In vain you make yourself beautiful, Unhealthy ones have kicked against you, They seek your life.
31 Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”
For I have heard a voice as of a travailing woman, Distress, as of one bringing forth a firstborn, The voice of the daughter of Zion, She laments herself, She spreads out her hands, Woe to me now, my soul is weary of slayers!”