< Irmiya 39 >

1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
Yahuda Kralı Sidkiya'nın dokuzuncu yılının onuncu ayında Babil Kralı Nebukadnessar bütün ordusuyla Yeruşalim önlerine gelerek kenti kuşattı.
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
Sidkiya'nın krallığının on birinci yılında, dördüncü ayın dokuzuncu günü kent surlarında gedik açıldı.
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
Yeruşalim ele geçirilince Babil Kralı'nın bütün komutanları –Samgarlı Nergal-Sareser, askeri danışman Nebo-Sarsekim, baş görevli Nergal-Sareser ve bütün öteki görevliler– içeri girip Orta Kapı'da oturdular.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
Yahuda Kralı Sidkiya'yla askerler onları görünce kaçtılar. Gece kral bahçesinin yolundan iki duvarın arasındaki kapıdan kaçarak Arava yoluna çıktılar.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
Ama artlarına düşen Kildani ordusu Eriha ovalarında Sidkiya'ya yetişti, onu yakalayıp Hama topraklarında, Rivla'da Babil Kralı Nebukadnessar'ın huzuruna çıkardılar. Nebukadnessar onun hakkında karar verdi:
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
Rivla'da Sidkiya'nın gözü önünde oğullarını, sonra da bütün Yahuda ileri gelenlerini öldürttü.
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
Sidkiya'nın gözlerini oydu, zincire vurup Babil'e götürdü.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
Kildaniler sarayla halkın evlerini ateşe verdiler, Yeruşalim surlarını yıktılar.
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
Komutan Nebuzaradan kentte sağ kalanları, kendi safına geçen kaçakları ve geri kalan halkı Babil'e sürgün etti.
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
Ancak hiçbir şeyi olmayan bazı yoksulları Yahuda'da bıraktı, onlara bağ ve tarla verdi.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
Babil Kralı Nebukadnessar, muhafız birliği komutanı Nebuzaradan aracılığıyla Yeremya'yla ilgili şu buyruğu verdi:
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
“Onu sorumluluğun altına al, ona iyi bak, hiç zarar verme, senden ne dilerse yap.”
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
Bunun üzerine muhafız birliği komutanı Nebuzaradan, askeri danışman Nebuşazban, baş görevli Nergal-Sareser ve Babil Kralı'nın öbür görevlileri
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
adam gönderip Yeremya'yı muhafız avlusundan getirttiler. Evine geri götürmesi için Şafan oğlu Ahikam oğlu Gedalya'nın koruyuculuğuna verdiler. Böylece Yeremya halkı arasında yaşamını sürdürdü.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Yeremya daha muhafız avlusunda tutukluyken RAB ona şöyle seslenmişti:
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
“Git, Kûşlu Ebet-Melek'e de ki, ‘İsrail'in Tanrısı, Her Şeye Egemen RAB şöyle diyor: Bu kent üzerine yarar değil, zarar verecek sözlerimi yerine getirmek üzereyim. O gün olanları sen de göreceksin.
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
Ama o gün seni kurtaracağım diyor RAB. Korktuğun adamların eline teslim edilmeyeceksin.
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
Seni kesinlikle kurtaracağım, kılıçla öldürülmeyeceksin. Hiç değilse canını kurtarmış olacaksın. Çünkü bana güvendin, diyor RAB.’”

< Irmiya 39 >