< Irmiya 39 >
1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
V devetem letu Judovega kralja Sedekíja, v desetem mesecu, je prišel babilonski kralj Nebukadnezar in vsa njegova vojska, zoper Jeruzalem in ga oblegal.
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
In v enajstem letu Sedekíja, v četrtem mesecu, devetega dne meseca, je bilo mesto predrto.
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
Vsi princi babilonskega kralja so vstopili in sedli v srednja velika vrata, celó Nergál Sarécer, Samgár Nebú, Sar Sehím, Rab-saris, Nergál Sarécer, Rab–mag, z vsem preostankom princev babilonskega kralja.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
Pripetilo se je, da ko so jih Judov kralj Sedekíja in vsi bojevniki zagledali, potem so zbežali in odšli naprej iz mesta ponoči po poti kraljevega vrta, ob velikih vratih med obema zidovoma, in odšel je ven po poti ravnine.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
Toda kaldejska vojska jih je zasledovala in Sedekíja dohitela na ravninah Jerihe. Ko so ga prijeli, so ga privedli gor k babilonskemu kralju Nebukadnezarju v Riblo, v Hamátovo deželo, kjer je ta podal razsodbo nad njim.
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
Potem je babilonski kralj usmrtil Sedekíjeve sinove v Ribli, pred njegovimi očmi. Prav tako je babilonski kraj usmrtil vse Judove plemiče.
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
Poleg tega je iztaknil Sedekíjeve oči in ga zvezal z verigami, da ga odvede v Babilon.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
Kaldejci so požgali kraljevo hišo in hiše ljudi z ognjem in porušili zidove Jeruzalema.
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
Potem je Nebuzaradán, poveljnik straže odvedel ujetništvo v Babilon, preostanek ljudstva, ki je ostal v mestu in tiste, ki so pobegnili proč, ki so prebegnili k njemu, s preostankom ljudstva, ki je preostalo.
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
Toda Nebuzaradán, poveljnik straže je pustil revne izmed ljudstva, ki niso imeli ničesar, v Judovi deželi in jim obenem dal vinograde in polja.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
Torej babilonski kralj Nebukadnezar je dal naročilo glede Jeremija Nebuzaradánu, poveljniku straže, rekoč:
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
»Vzemi ga in dobro glej nanj in ne stori mu ničesar hudega, temveč mu stori celo tako, kakor ti bo rekel.«
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
Tako je poslal Nebuzaradána, poveljnika straže, Nebušazbána, Rab-sarisa, Nergál Sarécerja, Rab-maga in vse kralje babilonskih princev;
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
celo oni so poslali in vzeli Jeremija z dvorišča ječe ter ga predali Gedaljáju, sinu Ahikáma, sinu Šafána, da bi ga odvedel domov. Tako je prebival med ljudstvom.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Torej beseda od Gospoda je prišla Jeremiju, medtem ko je bil zaprt na dvorišču ječe, rekoč:
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
»Pojdi in spregovori Etiopijcu Ebed Melehu, rekoč: ›Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog: ›Glej, svoje besede bom privedel nad to mesto v zlo in ne v dobro in le-te bodo na ta dan dovršene pred teboj.
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
Toda tebe bom na ta dan osvobodil, ‹ govori Gospod: ›in ne boš izročen v roko mož, ki se jih bojiš.
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
Kajti jaz te bom zagotovo osvobodil in ne boš padel pod mečem, temveč ti bo tvoje življenje za plen, ker si svoje zaupanje položil vame, ‹ govori Gospod.«