< Irmiya 39 >

1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
И бысть в девятое лето Седекии царя Иудина, в месяц десятый, прииде Навуходоносор царь Вавилонский и вся сила его на Иерусалим, и воеваху нань.
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
И в первоенадесять лето Седекии, в месяц четвертый, в девятый день месяца, разседеся град.
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
И внидоша вси князи царя Вавилонска и седоша во вратех средних, Ниргелсарасар, Самагад, Навусахар, Навусарис, Нагаргас, Насерравамаг, и прочии воеводы царя Вавилонскаго.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
И бысть егда узре я Седекиа царь Иудин и вси мужие ратнии, и избегоша, и изыдоша в нощи от града по пути вертограда царева и сквозе врата, яже беша между стеною и предстением: и изыдоша в путь пустыни.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
И гнаша вслед их воинство Халдейско, и постигоша Седекию и поли пустыни Иерихонския, и емше приведоша к Навуходоносору царю Вавилонску во Ревлаф, иже в земли Емаф, и глагола к нему с судом.
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
И изби царь Вавилонский сыны Седекиины во Ревлафе пред очима его, и вся вельможы Иудины поби царь Вавилонский.
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
И очи Седекии изят, и окова его путы, и отведе его в Вавилон.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
Дом же царев и домы всех людий пожгоша Халдее огнем и стену Иерусалимску превратиша:
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
и останок людий, и оставших во граде, и убегшыя, иже утекоша ко царю Вавилонску, и останок людий, и оставших пресели Навузардан воевода в Вавилон:
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
а от людий убогих, ничтоже имущих, остави Навузардан воевода воинств в земли Иудине, и даде им винограды и нивы в той день.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
И заповеда Навуходоносор царь Вавилонский о Иеремии пророце Навузарданови воеводе воинств и рече:
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
возми его и положи нань очи твои и ничтоже ему сотвори зла: но якоже восхощет, тако сотвори ему.
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
Посла убо Навузардан воевода воинства и Навузезван, и Рапсарис и Ниргел, и Сарасар и Фавман, и вси воеводы царя Вавилонска:
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
и послаша, и пояша Иеремию от двора темничнаго, и даша его Годолии сыну Ахикамову, сына Сафаня, и изведоша его, и седе среде людий.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
И ко Иеремии бысть слово Господне ко дворе темничнем глаголя:
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
иди и рцы ко Авдемелеху Мурину, глаголя: тако рече Господь Бог Израилев: се, Аз приношу словеса Моя на град сей во злая? А не во благая: и будут пред лицем твоим в той день:
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
и избавлю тя в той день, и не дам тебе в руце человек, ихже ты боишися от лица их:
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
яко избавляя спасу тя, и мечем не падеши: и будет душа твоя на обретение, яко уповал еси на Мя, рече Господь.

< Irmiya 39 >