< Irmiya 39 >

1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
La neuvième année de Sédécias, roi de Juda, au dixième mois, Nabuchodonosor, roi de Babylone, vint et toute son armée devant Jérusalem, et ils en faisaient le siège.
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
Mais la onzième année de Sédécias, au quatrième mois, le cinquième jour, la cité fut ouverte.
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
Et tous les princes du roi de Babylone entrèrent, et se postèrent à la porte du milieu: Nérégel, Séréser, Sémégarnabu, Sarsachim, Rabsarès, Nérégel, Séréser, Rebmag, et tous les autres princes du roi de Babylone.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
Et lorsque Sédécias, roi de Juda, et tous les hommes de guerre les eurent aperçus, ils s’enfuirent; et ils sortirent la nuit de la cité par la voie du jardin du roi, et par la porte qui était entre les deux murs, et ils se dirigèrent vers la voie du désert.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
Mais l’armée des Chaldéens les poursuivit; et ils prirent Sédécias dans les champs de la solitude de Jéricho, et ils l’amenèrent prisonnier à Nabuchodonosor, roi de Babylone, à Réblatha qui est en la terre d’Emath; et Nabuchodonosor lui prononça son arrêt.
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
Et le roi de Babylone fit mourir les deux fils de Sédécias à Réblatha, sous ses yeux, et tous les nobles de Juda, le roi de Babylone les fit mourir.
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
Il arracha aussi les yeux à Sédécias, et le chargea de fers aux pieds, afin qu’il fût emmené à Babylone.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
Les Chaldéens mirent aussi le feu à la maison du roi et aux maisons du peuple, et ils renversèrent le mur de Jérusalem.
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
Et les restes du peuple qui étaient demeurés dans Jérusalem, et les transfuges qui s’étaient réfugiés auprès de lui, et les restants du peuple qui étaient demeurés, Nabuzardan, chef de la milice, les transféra à Babylone.
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
Et quant à la foule des pauvres qui ne possédaient absolument rien, Nabuzardan, chef de la milice, la laissa dans la terre de Juda et lui donna des vignes et des citernes en ce jour-là.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
Mais Nabuchodonosor, roi de Babylone, avait donné à Nabuzardan, chef de la milice, cet ordre touchant Jérémie, disant:
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
Prends-le et tiens sur lui tes yeux, et ne lui fais aucun mal: mais comme il voudra, ainsi tu lui feras.
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
Nabuzardan donc, chef de la milice, envoya, et Nabusezban, et Rabsarès, et Nérégel, et Séréser, et Rebmag, et tous les autres grands du roi de Babylone,
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
Envoyèrent et firent sortir Jérémie du vestibule de la prison, et ils le remirent à Godolias, fils d’Ahicam, fils de Saphan, afin qu’il entrât dans une maison et qu’il habitât au milieu du peuple.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Mais à Jérémie avait été adressée la parole du Seigneur, lorsqu’il était enfermé dans le vestibule de la prison, disant:
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
Va, et parle à Abdémélech l’Ethiopien, disant: Voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: Voilà que j’amènerai mes paroles sur cette cité, pour son mal, et non pour son bien: elles auront lieu en ce jour-là devant tes yeux.
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
Et je te délivrerai, en ce jour-là, dit le Seigneur; et tu ne seras pas livré aux mains des hommes que tu redoutes;
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
Mais, t’en retirant, je te délivrerai, et tu ne tomberas pas sous le glaive; mais ta vie te sera sauvée, parce que tu as eu confiance en moi, dit le Seigneur.

< Irmiya 39 >