< Irmiya 39 >

1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
La neuvième année de Sédécias, roi de Juda, au dixième mois, Nebucadnetsar, roi de Babylone, et toute son armée vinrent contre Jérusalem et l'assiégèrent.
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
La onzième année de Sédécias, le quatrième mois, le neuvième jour du mois, une brèche fut ouverte dans la ville.
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
Tous les princes du roi de Babylone entrèrent et s'assirent à la porte du milieu: Nergal Sharezer, Samgarnebo, Sarsechim, le Rabsaris, Nergal Sharezer, le Rabmag, et tous les autres princes du roi de Babylone.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
Lorsque Sédécias, roi de Juda, et tous les hommes de guerre les virent, ils s'enfuirent et sortirent de nuit de la ville, par le chemin du jardin du roi, par la porte entre les deux murs.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
Mais l'armée des Chaldéens les poursuivit et rattrapa Sédécias dans les plaines de Jéricho. Après l'avoir pris, ils le firent monter devant Nebucadnetsar, roi de Babylone, à Ribla, dans le pays de Hamath, et il prononça un jugement contre lui.
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
Alors le roi de Babylone tua sous ses yeux les fils de Sédécias à Ribla. Le roi de Babylone tua aussi tous les nobles de Juda.
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
Il fit crever les yeux à Sédécias et le lia avec des chaînes, pour le transporter à Babylone.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
Les Chaldéens incendièrent la maison du roi et les maisons du peuple et démolirent les murailles de Jérusalem.
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
Alors Nebuzaradan, chef des gardes, emmena captifs à Babylone le reste du peuple qui était resté dans la ville, les déserteurs qui s'étaient ralliés à lui, et le reste du peuple qui était resté.
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
Mais Nebuzaradan, chef des gardes, laissa dans le pays de Juda les pauvres du peuple, qui n'avaient rien, et leur donna en même temps des vignes et des champs.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
Nebucadnetsar, roi de Babylone, donna cet ordre à Nebuzaradan, chef des gardes, au sujet de Jérémie:
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
« Prends-le et occupe-toi de lui. Ne lui fais pas de mal, mais fais-lui ce qu'il te dira. »
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
Alors Nebuzaradan, chef des gardes, Nebushazban, Rabsaris, Nergal Sharezer, Rabmag, et tous les officiers supérieurs du roi de Babylone
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
envoyèrent chercher Jérémie dans la cour des gardes, et le confièrent à Guedalia, fils d'Ahikam, fils de Shaphan, pour qu'il le ramène chez lui. Il vécut ainsi parmi le peuple.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
La parole de Yahvé fut adressée à Jérémie, pendant qu'il était enfermé dans la cour des gardes, en ces termes:
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
Va, et dis à Ebed Melech, l'Éthiopien, que Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Voici, je ferai venir sur cette ville mes paroles en mal et non en bien, et elles s'accompliront devant toi en ce jour-là.
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
Mais je te délivrerai en ce jour-là, dit l'Éternel, et tu ne seras pas livré entre les mains des hommes dont tu as peur.
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
Car je te sauverai. Tu ne tomberas pas par l'épée, mais tu t'échapperas avec ta vie, parce que tu as mis ta confiance en moi, dit Yahvé.'"

< Irmiya 39 >