< Irmiya 39 >

1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
And it came to pass when Jerusalem was taken, in the ninth year of Zedekiah king of Judah, in the tenth month, Nebuchadrezzar king of Babylon and all his army came against Jerusalem, and besieged it.
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
In the eleventh year of Zedekiah, in the fourth month, the ninth day of the month, a breach was made in the city.
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
And all the princes of the king of Babylon came in, and sat in the middle gate, to wit, Nergal-sharezer, Samgar-nebo, Sarsechim, Rab-saris, Nergal-sharezer, Rab-mag, with all the rest of the princes of the king of Babylon.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
And it came to pass that, when Zedekiah the king of Judah and all the men of war saw them, then they fled, and went forth out of the city by night, by the way of the king's garden, through the gate between the two walls, and he went out toward the Arabah.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
But the army of the Chaldeans pursued after them, and overtook Zedekiah in the plains of Jericho. And when they had taken him, they brought him up to Nebuchadrezzar king of Babylon to Riblah in the land of Hamath, and he gave judgment upon him.
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
Then the king of Babylon killed the sons of Zedekiah in Riblah before his eyes. Also the king of Babylon killed all the nobles of Judah.
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
Moreover he put out Zedekiah's eyes, and bound him in fetters to carry him to Babylon.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
And the Chaldeans burned the king's house, and the houses of the people, with fire, and broke down the walls of Jerusalem.
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
Then Nebuzaradan the captain of the guard carried away captive into Babylon the residue of the people that remained in the city, the deserters also that fell away to him, and the residue of the people that remained.
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
But Nebuzaradan the captain of the guard left of the poor of the people, that had nothing, in the land of Judah, and gave them vineyards and fields at the same time.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
Now Nebuchadrezzar king of Babylon gave charge concerning Jeremiah to Nebuzaradan the captain of the guard, saying,
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
Take him, and look well to him, and do him no harm, but do to him even as he shall say to thee.
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
So Nebuzaradan the captain of the guard sent, and Nebushazban, Rab-saris, and Nergal-sharezer, Rab-mag, and all the chief officers of the king of Babylon.
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
And they sent, and took Jeremiah out of the court of the guard, and committed him to Gedaliah the son of Ahikam, the son of Shaphan, that he should carry him home. So he dwelt among the people.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Now the word of Jehovah came to Jeremiah while he was shut up in the court of the guard, saying,
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
Go, and speak to Ebed-melech the Ethiopian, saying, Thus says Jehovah of hosts, the God of Israel: Behold, I will bring my words upon this city for evil, and not for good, and they shall be accomplished before thee in that day.
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
But I will deliver thee in that day, says Jehovah, and thou shall not be given into the hand of the men of whom thou are afraid.
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
For I will surely save thee, and thou shall not fall by the sword, but thy life shall be for a prey to thee, because thou have put thy trust in me, says Jehovah.

< Irmiya 39 >