< Irmiya 39 >

1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
Efter at Jerusalem var indtaget — i Kong Zedekias af Judas niende Regeringsaar i den tiende Maaned, kom Kong Nebukadrezar af Babel med hele sin Hær til Jerusalem og belejrede det;
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
i Zedekias's ellevte Aar paa den niende Dag i den fjerde Maaned blev Byen stormet —
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
da kom alle Babels Konges Fyrster og satte sig i Midterporten: Overhofmanden Nebusjazban, Magernes Øverste Nergal-Sar'ezer og alle Babels Konges andre Fyrster.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
Da Kong Zedekias af Juda og alle hans Krigsmænd saa dem, flygtede de om Natten fra Byen ad Vejen til Kongens Have gennem Porten mellem de to Mure og tog Vejen ad Araba til.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
Men Kaldæernes Hær satte efter dem og indhentede Zedekias paa Jerikos Lavslette; og de tog ham med og bragte ham op til Kong Nebukadnezar af Babel i Ribla i Hamats Land; og han fældede hans Dom.
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
Babels Konge lod i Ribla Zedekias's Sønner dræbe i hans Paasyn; ogsaa alle de ypperste i Juda lod Babels Konge dræbe;
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
derpaa lod han Øjnene stikke ud paa Zedekias og lod ham lægge i Kobberlænker for at føre ham til Babel.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
Kaldæerne satte Ild paa Kongens Palads og Folkets Huse og nedbrød Jerusalems Mure.
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
Resten af Folket, der var levnet i Byen, Overløberne, der var løbet over til ham, og Resten af Haandværkerne førte Livvagtsøversten Nebuzar'adan som Fanger til Babel,
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
og kun nogle af den fattigste Befolkning, der intet ejede, lod Livvagtsøversten Nebuzar'adan blive tilbage i Judas Land, idet han samtidig gav dem Vingaarde og Agre.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
Men om Jeremias bød Kong Nebukadrezar af Babel Livvagtsøversten Nebuzar'adan:
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
»Tag ham og hav Øje med ham og gør ham ingen Men; gør med ham, som han selv ønsker!«
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
Saa sendte Livvagtsøversten Nebuzar'adan, Overhofmanden Nebusjazban og Magernes Øverste Nergal-Sar'ezer og alle Babels Konges andre Stormænd
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
Bud og lod Jeremias hente i Vagtforgaarden og overgav ham til Gedalja, en Søn af Sjafans Søn Ahikam, for at han skulde føre ham til hans Hjem; og han boede iblandt Folket.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Medens Jeremias sad fængslet i Vagtforgaarden, kom HERRENS Ord til ham saaledes:
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
Gaa hen og sig til Ætioperen Ebed-Melek: Saa siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: Se, jeg lader mine Ord gaa i Opfyldelse paa denne By til Ulykke og ikke til Lykke, og du skal have dem i Tankerne paa hin Dag.
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
Men paa hin Dag redder jeg dig, lyder det fra HERREN, og du skal ikke gives i de Mænds Haand, for hvem du frygter;
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
thi jeg vil frelse dig, saa du ikke falder for Sværdet, og du skal vinde dit Liv som Bytte, fordi du stolede paa mig, lyder det fra HERREN.

< Irmiya 39 >